PDP Ta Sake Birkicewa, Sanata Ya Sauya Sheka zuwa Jam'iyyar APC

PDP Ta Sake Birkicewa, Sanata Ya Sauya Sheka zuwa Jam'iyyar APC

  • ​​Sanata mai wakiltar yankin Kudancin jihar Kaduna a majalisar dattawa ya tabbatar da sauya shekarsa daga jam’iyyar adawa
  • A yanzu Sunday Marshall Katung ya rabu da jam’iyyar PDP, ya shiga APC mai rinjaye a majalisar wakilai da dattawan Najeriya
  • ‘Dan siyasar ya raba gari da PDP da ta ba shi damar zama Sanata, ‘dan majalisar wakilai da kuma ‘dan takara a zaben gwamna

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Sanata mai wakiltar Kaduna ta Kudu a majalisar dattawa, Sunday Marshall Katung, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP.

Sanata Sunday Marshall Katung ya kuma sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Sanata Sunday Marshall Katung ya koma jam'iyyar APC
Sanata Sunday Marshall Katung mai wakiltar Kaduna ta Kudu Hoto: @smkatung
Source: Twitter

Jaridar Tribune ta kawo rahoton cewa an karanta wasikar sauya shekar Sanata Sunday ne a gaban Majalisar Dattawa a ranar Laraba, 17 ga watan Disamban 2025.

Kara karanta wannan

Jita jitar mutuwar Akpabio ta harzuka majalisa, ta dauki mataki

Shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya karanta wasikar ga sanatoci yayin zaman majalisar.

A cikin wasikar, Sanata Marshall Katung ya ce PDP ta shiga tsaka mai wuya na rarrabuwar kai, tare da cewa jam’iyyar ba ta dace da muradun masu kada kuri’a a mazabarsa ba.

Meyasa Katung ya fice daga PDP zuwa APC?

Ya kuma ce “canjin yanayin siyasa” da ke faruwa a Najeriya ya nuna a fili cewa tabbatar da makomar siyasa a gareshi da mutanen da yake wakilta na tare ne da jam’iyyar APC.

“Ina so na tabbatar a hukumance da shawarar da na yanke na yin murabus daga kasancewa mamba na jam'iyyar PDP, daga ranar 31 ga watan Oktoba, 2025."
“Wannan shawara, duk da cewa an yi ta ne bayan zurfin tunani, ba a dauke ta da wasa ba."
“Tsawon shekaru, na tsaya tsayin daka wajen bin ka’idojin dimokuradiyya, shugabanci nagari da hidima ga al’umma, waɗanda PDP ke wakilta a wancan lokaci."

Kara karanta wannan

Manyan badakalolin siyasa 5 da suka faru a shekarar 2025 a Najeriya

“Amma sauye-sauyen siyasa da ke faruwa a kasar nan da kuma a mazabata sun tilasta sake nazari kan PDP da kuma tantance wace jam’iyya ce ta fi dacewa da ni wajen cimma burina na kula da jama’ata da walwalarsu.”

- Sanata Sunday Marshall Katung

Sanata Katung ya yabi jam'iyyar APC

Sanata Katung ya ce bayan tattaunawa mai zurfi da masu ruwa da tsaki, magoya baya da ’yan Najeriya masu kishin ƙasa, ya yanke shawarar daidaita kansa da jam’iyyar APC, jaridar TheCable ta dauko labarin.

Ya bayyana APC a matsayin wata jam’iyya da alkiblarta da shugabancinta a halin yanzu ke bayar da sabon buri, haɗin kai, kwanciyar hankali da ci gaba mai ɗorewa.

“Shawarata ta ta’allaka ne kawai a kan yi wa mazabata da kasa hidima yadda ya kamata. Babu ɗan siyasar da zai so ya katse burinsa na siyasa ko kuma makomarsa ta siyasa."

Sanata Sunday Marshall Katung

Sanata Sunday Marshall Katung ya sauya sheka daga PDP zuwa APC
Sanata Sunday Marshall Katung a zauren majalisar dattawa Hoto: @smkatung
Source: Facebook

Sanata Katung ya kuma godewa PDP

Sanata Katung ya ce yana matuƙar godiya bisa damar da jam’iyyar PDP ta ba shi tsawon shekarun da suka gabata, tare da yi wa jam’iyyar fatan alheri a dukkan ayyukanta na gaba.

Bayan karanta wasikar, Shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Opeyemi Bamidele, ya jagoranci Sanata Katung da sauran sanatocin APC zuwa wajen shugaban majalisa, Godswill Akpabio, domin ɗaukar hoto.

Kara karanta wannan

"Ba zan taba komawa APC ba," Sanata ya yi kaca kaca da gwamnoni 6 a Najeriya

Daga nan aka raka Sanata Katung zuwa kujerarsa a layin masu rinjaye a zauren majalisar.

Gwamna Makinde ba zai koma APC ba

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya yi magana kan komawa jam'iyyar APC.

Gwamna Seyi Makinde ya bayyana cewa ba zai sauya sheka daga jam'iyyarsa ta PDP zuwa APC mai mulki ba.

Kalaman Gwamna Makinde na zuwa ne yayin da wasu gwamnonin PDP ke rububin sauya sheka zuwa jam'iyyar APC.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng