Mutuwa Mai Yankar Kauna: An Tabbatar da Rasuwar Tsohon Jagora a NLC ta Kasa

Mutuwa Mai Yankar Kauna: An Tabbatar da Rasuwar Tsohon Jagora a NLC ta Kasa

  • Kungiyar NLC ta tabbatar da rasuwar tsohon sakatarenta na kasa, Peter Ozo-Esan a asibitin UCH da ke Ibadan, babban birnin jihar Oyo
  • NLC ta bayyana marigayin a matsayin dan gwagwarmaya, wanda ya ba da gudummuwa matuka wajen kare hakkin ma'aikata a Najeriya
  • Ozo-Eson ya hau kujerar sakataren NLC a watan Agustan 2014, bayan hukuncin da Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (NEC) ta kungiyar ta yanke

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Oyo, Nigeria - Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta rasa daya daga cikin manyan jagororin da suka rike mukamai a baya.

Tsohon Sakatare Janar na Ƙungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), Peter Ozo-Eson, ya riga mu gidan gaskiya a jihar Oyo da ke Kudancin Najeriya.

Peter Ozo-Eson.
Tsohon sakataren kungiyar NLC ta kasa, Peter Ozo-Eson Hoto: NLC HQ
Source: Facebook

Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa 'dan tsohon sakataren NLC na kasa ne ya tabbatar da rasuwar mahaifinsa a wata sanarwa da ya fitar jiya Litinin, 15 ga watan Disamba, 2025.

Kara karanta wannan

NNPCL: Bututun mai ya yi bindiga, ya kama da wuta a Delta

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

NLC ta tabbatar da rasuwar Uzo-Eson

Haka zalika, Ƙungiyar Kwadago ta NLC ta sanar da rasuwar ta sa a wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook.

NLC ta bayyana cewa marigayi Ozo-Eson ya rasu ne a ranar Lahadi, 14 ga watan Disamba, 2025 a Asibitin University College Hospital (UCH) da ke Ibadan, babban birnin Oyo.

“Ƙungiyar Kwadago ta Najeriya na sanar da rasuwar tsohon Sakataren Janar na ƙungiyar, Kwamared (Dr.) Peter Ozo-Eson, cikin matuƙar alhini."
"Ba za mu taba manta wa da kwazonsa, basira da sadaukarwar da ya yi ta tsawon lokaci wajen kare muradun ma’aikata da gwagwarmayar ƙwadago a Najeriya ba, ba za a iya goge gudummuwar da ya bayar ba.
“Za a yi kewarsa matuƙa tun daga Ƙungiyar Kwadago, ma'aikata baki ɗaya, da dukkan waɗanda suka yi tarayya da shi wajen burinsa na gina adalci da daidaito a cikin al’umma,” in ji sanarwar NLC.

Kara karanta wannan

NLC: 'Yan kwadago sun saka ranar zanga zanga a jihohi 36 da Abuja

Takaitaccen bayani kan tsohon sakataren na NLC

An naɗa Ozo-Eson a matsayin Sakataren NLC a watan Agustan 2014, bayan hukuncin da Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (NEC) ta ƙungiyar ta yanke a taronta da ya gudanar a jihar Enugu.

Kafin naɗinsa a wannan matsayi, marigayi Peter Ozo-Eson ya riƙe muƙamin Babban Masanin Tattalin Arziki na NLC tare da shugabancin sashen bincike na ƙungiyar.

Ya bar ofis a shekarar 2019 bayan kammala wa’adinsa, inda Emmanuel Ugboaja ya gaje shi.

Kungiyar NLC.
Tambarin kungiyar NLC da tsohon sakatarenta na kasa, Peter Ozo-Eson Hoto: NLC HQ
Source: Facebook

Ƙungiyar NLC ta kara da cewa za a fitar da sanarwar karin bayani game da shirye-shiryen jana'izar marigayin nan ba da dadewa ba.

Tsohon jakadan Najeriya ya rasu

A wani rahoton, kun ji cewa kungiyar IEDPU ta tabbatar da rasuwar tsohon shugabanta kuma tsohon jakadan Najeriya a kasar China, Sheikh Uthman AbdulAzeez.

An ruwaito cewa AbdulAzeez ya rasu yana da shekaru 71 a daren ranar Asabar, 13 ga watan Disamba, 2025 bayan gajeriyar rashin lafiya.

Kara karanta wannan

EFCC ta fara shari'a da ministan Buhari a kotu kan tuhume tuhumen rashawa 8

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, da tsohon shugaban Majalisar dattawa, Sanata Abubakar Bukola Saraki sun mika sakon ta'aziyya ga iyalan marigayin.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262