Tinubu Ya Sa Labule da Hafsoshin Tsaro bayan Amincewa da Tura Sojoji Benin

Tinubu Ya Sa Labule da Hafsoshin Tsaro bayan Amincewa da Tura Sojoji Benin

  • Mai girma Bola Ahmed Tinubu ya kira manyan hafsoshin tsaro zuwa fadar shugaban kasa da ke Aso Rock Villa a birnin tarayya Abuja
  • Shugaban kasat ya sanya labule da hafsoshin tsaron da Yammacin ranar Litinin, 15 ga watan Disamban 2025, inda suka tattauna muhimman batutuwa
  • Ganawar ta su dai na zuwa ne yayin da ake ci gaba da kokarin samo hanyoyin da za a kawo karshen matsalolin rashin tsaro da suka addabi 'yan Najeriya

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya shiga ganawa da manyan hafsoshin tsaron kasa.

Shugaba Tinubu na gudanar da taron na sirri ne da manyan hafsoshin tsaro a fadar shugaban kasa da ke fadar Aso Rock, a birnin tarayya Abuja.

Shugaba Tinubu ya gana da hafsoshin tsaro
Shugaba Bola Tinubu tare da hafsoshin tsaro Hoto: @aonauga1956
Source: Twitter

Jaridar The Punch ta kawo rahoton cewa taron ya fara ne da misalin karfe 6:01 na yammacin ranar Litinin, 15 ga watan Disamban 2025.

Kara karanta wannan

Ministan tsaro ya tsage gaskiya kan matsalar rashin tsaro a Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya gana da hafsoshin tsaro

Hafsoshin tsaron sun isa harabar fadar kafin a rakasu zuwa ofishin shugaban kasa.

Rahoton Daily Post ya nuna cewa wannan shi ne taron farko da Tinubu ke yi da manyan shugabannin sojoji tun bayan rantsar da Janar Christopher Musa (mai ritaya) a matsayin sabon Ministan Tsaro a ranar 4 ga watan Disamba.

Duk da cewa ajandar taron na ranar Litinin ba a bayyana ta ba a hukumance, ana gudanar da ganawar ne yayin da dalibai 115 da aka sace daga wata makarantar kwana ta Katolika a watan Nuwamba har yanzu ke hannun masu garkuwa da mutane.

Ana samun matsalolin rashin tsaro

A ranar 26 ga watan Nuwamba, Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan tsaron kasa tare da ba da umarnin daukar sababbin jami’ai a hukumomin tsaro.

Haka kuma, ya bayar da umarnin janye dukkan ’yan sandan da ke aiki a matsayin masu tsaron manyan mutane (VIPs).

Kara karanta wannan

Da gaske Tinubu na amfani da EFCC wajen kama 'yan adawa a Najeriya?

Taron ya zo ne ’yan kwanaki bayan Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da bukatar Tinubu ta tura sojoji zuwa Jamhuriyar Benin, biyo bayan yunkurin juyin mulki da aka yi a kasar.

Shugaba Tinubu ya gana da hafsoshin tsaro
Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu Hoto: @DOlusegun
Source: Facebook

Karanta wasu labaran kan Tinubu

Tinubu ya yi ta'aziyyar mataimakin gwamnan Bayelsa

A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna jimaminsa kan rasuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo.

Shugaba Tinubu ya mika sakon ta'aziyyarsa ga gwamnati da al’ummar jihar Bayelsa kan rasuwar marigayin wanda ya yi bankwana da duniya.

Mai girma Tinubu ya bayyana marigayi Ewhrudjakpo a matsayin jajirtaccen mutum mai gaskiya da rikon amana, wanda ya yi wa jihar Bayelsa da Najeriya hidima cikin kishin kasa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng