Hankula Sun Tashi, Mataimakin Gwamna Ya Fadi a Ofis, an Wuce da Shi Asibiti

Hankula Sun Tashi, Mataimakin Gwamna Ya Fadi a Ofis, an Wuce da Shi Asibiti

  • An shiga firgici bayan mataimakin gwamnan ya fadi a cikin ofishinsa lamarin da ya tayar da hankula a tsakanin masoyansa
  • Majiyoyi sun ce Sanata ya fadi yayin da aka yi gaggawar garzayawa da shi asibiti domin ceto lafiyarsa cikin gaggawa
  • 2. Likitoci sun tabbatar da an kwantar da shi a ICU, yayin da hukumomi suka ce har yanzu ba a bayyana musabbabin matsalar ba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Yenagoa, Bayelsa - Fargaba ta mamaye birnin Yenagoa, babban birnin jihar Bayelsa game da lafiyar mataimakin gwamna.

Rahotanni sun nuna cewa Mataimakin Gwamna, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo, ya fadi cak a ofishinsa a yau Alhamis 11 ga watan Disambar 2025.

Mataimakin gwamna ya fadi a ofishinsa
Gwamnan Bayelsa, Douye Diri da mataimaikinsa. Hoto: Douye Diri.
Source: Twitter

Mataimakin gwamnan Bayelsa ya fadi a ofishinsa

Rahoton Vanguard ya tabbatar da cewa dan siyasar yana cikin wani hali yayin da aka kuma garzaya da shi asibitin gwamnatin tarayyada ke Yenagoa.

Kara karanta wannan

Abin da Kiristoci suka fadawa dan majalisar Amurka da ya ziyarce su a Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Lamarin ya faru ne kusan ƙarfe 1:30 na rana a yayin da yake aiki a ofishinsa, lamarin da ya sa an kira gaggawa.

Shaidu sun ce halin da yake ciki ya yi muni sosai lokacin da aka kai shi sashen gaggawa na asibitin.

Wane hali mataimakin gwamnan ke ciki

Sanata Ewhrudjakpo yanzu haka an kwantar da shi a sashen kula da numfashi (ICU) inda likitoci ke kula da shi.

Har yanzu babu wata sanarwa ta hukuma game da musabbabin matsalarsa, sai dai majiyoyi sun ce yana iya kasancewa matsalar zuciya ce.

Wata majiya mai kusanci da shi ta ce yana da yawan aiki matuka, tana mai cewa:

"Mutumin mai aiki ne sosai; yakamata ya rika samun lokaci ya huta."

Jami’an tsaro sun mamaye asibitin, yayin da manyan jami’an gwamnati suka ziyarce shi domin nuna damuwa.

Kokarin da aka yi don jin ta bakin mai magana da yawun mataimakin gwamnan, Mista Doubara Atasi, ya ci tura.

Kara karanta wannan

'Na gama yin shiru,' Matawalle ya tona wadanda ke daukar nauyin bata masa suna

Sai dai majiyoyin asibiti sun tabbatar cewa yana samun cikakkiyar kulawa kuma yanayin da yake ciki ya fara daidaituwa.

Mataimakin gwamna na kwance a asibiti bayan ya fadi a ofi
Mataimakin gwamnan Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo. Hoto: Sen. Lawrence Ewhrudjakpo.
Source: Twitter

Ana jita-jitar sanadin faduwar mataimakin gwamna

An tabbatar da cewa lamarin ya tayar da hankula duba da halin da aka gano shi a cki bayan yafadi kafin a wuce da shi asibiti domin ceto lafiyarsa cikin gaggawa.

Wadanda suka san sanatan sun bayyana cewa mutum ne jajitacce a wurin aiki wanda bai gajiya, mafi yawansu ma su na danganta hakan da sanadin faduwarsa.

Har ila yau, gwamnatin jihar ba ta ce komaiba har zuwa lokacin tattara wannan rahoto saboda Wakilin Legit Hausa ya ziyarci shafukan sanatan da kuma na gwamnan jihar amma babu wata sanarwa.

Minista ya fadi yayin tantance shi a majalisa

Kun ji cewa Minista Balarabe Abbas ya bayyana dalilin faduwarshi a majalisar Dattawa yayin da ake tantance shi a birnin tarayya Abuja.

Balarabe wanda shi ne ya maye gurbin El-Rufai daga jihar Kaduna ya suma ana tsaka da tantance shi domin ba shi kujerar minista.

Kara karanta wannan

Najeriya ta janye jirgin yakinta zuwa Benin bayan sanin halin da ake ciki

Ya bayyana wa shugaban majalisar, Goswill Akpabio cewa ya shafe kwanaki uku ya na aiki ba tare da hutawa ba wanda ya ce shi ne sanadin sumar da ya yi a majalisar.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.