An Yi Wa Babban Dan Sanda Dukan Kawo Wuka kan Zargin Sata? Rundunar Ta Magantu

An Yi Wa Babban Dan Sanda Dukan Kawo Wuka kan Zargin Sata? Rundunar Ta Magantu

  • Rundunar ‘yan sanda ta Lagos ta yi magana kan wani bidiyo da ya karade kafofin sadarwa game da jami'inta
  • An yada bidiyo ne cewa an kama dan sandan yana sata, tana bayyana cewa an kai masa hari ne yayin aiki
  • An kama mutane 13 da suka lakada wa jami’in duka, yayin da rundunar ta gargadi jama’a kan kai hari ga jami’an tsaro

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ikeja, Lagos - Rundunar ‘yan sandan Lagos ta fitar da sanarwa game da dukan wani jami'inta da aka yi a jihar.

Rundunar ta musanta wani bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta cewa an yi wa jami'in duka saboda ya yi sata.

An karyata cewa babban dan sanda ya yi sata a Lagos
Sufeta-janar na yan sanda, Kayode Egbetokun da dan sanda da aka yi wa duka a Lagos. Hoto: Nigeria Police Force.
Source: Facebook

Matasa sun lakadawa dan sanda duka

Legit Hausa ta samu wannan martani ne daga shafin rundunar wanda ta wallafa a manhajar X a yau Alhamis 11 ga watan Disambar 2025.

Kara karanta wannan

Sanata ya yi kumfar baki a majalisa bayan janye masa 'yan sanda

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An yada bidiyon ne cewa wani jami’in ‘yan sanda ana bugunsa ne kan zargin yana sata, inda ta bayyana cewa an kai masa hari ne yayin da yake kan aiki.

A cikin sanarwar, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Abimbola Adebesi ya ce bayanan da aka haɗa da bidiyon “karya ne kuma yaudara,” domin an juya gaskiyar lamarin ta hanyar yada jita-jita.

Rundunar ta ce jami’in da abin ya shafa inspekta ne da ke aiki a karkashin hukumar kula da ababen hawa ta Lagos, kuma yana aiwatar da dokar haramta ajiye motoci ba bisa ka’ida ba a titin Brown, Oshodi, lokacin da rikicin ya faru.

Wasu matasa sun yi wa babban dan sanda duka a Lagos
Sufeta-janar na yan sanda, Kayode Egbetokun. Hoto: Nigeria Police Force.
Source: Facebook

Yadda rigima ta barke da dan sanda

Jami’in ya dakatar da wani direba da ke ƙoƙarin ajiye mota bisa saba doka, sai dai direban ya mayar lamarin na tashin hankali.

A lokacin rikicin, inspektan ya yi harbi a ƙasa ba da gangan ba, wanda ya jawo hankulan wasu mutane da ke wucewa.

Kara karanta wannan

Abin da Kiristoci suka fadawa dan majalisar Amurka da ya ziyarce su a Najeriya

Wannan ya jawo taruwar mutane, inda aka dinga lakada masa duka har ya samu munanan raunuka.

Sanarwar ta ƙara da cewa ko da yake an ɗauki matakin ladabtarwa kan inspektan saboda rashin da’a, rundunar ta riga ta kama mutum 13 da aka gani a bidiyon suna bugunsa.

Kwamishinan ‘yan sandan Lagos ya yi Allah-wadai da yadda inspektan ya yi rashin da’a, amma ya yi gargaɗi mai tsanani kan hare-hare ga jami’an tsaro yayin da suke gudanar da ayyukansu na doka, yana mai cewa hakan babban laifi ne.

Yan sanda sun kama yan fashi a Lagos

An ji cewa rundunar 'yan sandan Najeriya a jihar Lagos ta kama mutane 35 da ake zargi da fashi da makami a titi a yankunan Ajah da Elemoro.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an kama su ne a yayin atisayen sintiri da jami'an tsaro suka kaddamar don dakile ayyukan masu laifi.

Kakakin 'yan sandan jihar ya ce ana ci gaba da kai irin wadannan farmaki a jihar don tabbatar da doka da oda da maganain bata gari.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.