Abin da Kwankwaso Ya Fadawa Gwamna Abba da Mukarrabansa a Abuja
- Jagoran NNPP na kasa kuma tsohon dan takarar shugaban kasa, Rabiu Musa Kwankwaso ya karbi bakuncin Gwamna Abba da mukarrabansa
- Gwamna Abba ya kai wa Kwankwaso ziyara har gida a Abuja domin nuna masa lambar yabon da aka ba shi saboda kyakkyawan jagoranci
- Kwankwaso ya yabawa gwamnan bisa irin ci gaba da Kano ke samu karkashin jagirancinsa, ya ce yana alfahari da hakan
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya jagoranci tawagar gwamnatin Kano, sun kai ziyara gidan jagoran NNPP na kasa, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso.
Tawagar gwamnatin Kano ta kai wannan ziyara ta girmamawa ga tsohon gwamnan da ke babban birnin tarayya Abuja ranar Lahadi, 7 ga watan Disamba, 2025.

Source: Facebook
Kwankwaso, tsohon dan takarar shugaban kasa a inuwar jam'iyyar NNPP ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook yau Litinin.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Me ya kai Gwamna Abba gidan Kwankwaso?
Tsohon gwamnan kuma jagoran NNPP ya bayyana cewa ya karɓi bakuncin mai girma gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, a gidansa da ke Abuja.
Bayanai sun nuna cewa gwamnan ya je tare da tawagar gwamnatinsa domin nuna wa Kwankwaso lambar girmamawa da aka ba shi a taron NEAPS da aka gudanar a Abuja.
An dai bai wa Gwamna Abba lambar yabo ta “Distinguished Award for Visionary Leadership and Public Service Sector Reform”, bisa sauyin da ya kawo da kuma kyakkawan jagorancin da ya kafa a Kano.
Abin da Kwankwaso ya fadawa Abba
Kwankwaso ya taya Gwamna Abba murna bisa wannan gagarumar nasara da ya samu, yana mai jinjina ci gaban da jihar Kano ke samu a karkashin jagorancinsa.
Madugun Kwankwasiyya ya ce:
"Ina taya Gwamna Abba murna bisa wannan nasara. Ina alfahari da irin kwararan matakai da ci gaba da Kano ke samu a ƙarƙashin jagorancinsa.”

Source: Facebook
Jigon NNPP ya yaba wa jiga-jigan 2
Wani dan Kwankwasiyya, Sa'idu Abdu ya shaidawa Legit Hausa cewa irin wannan kyakkywar alaka da mutunta juna ne wasu 'yan adawa ba su son gani tsakanin Kwankwaso da Abba.
Jigon NNPP ya taya Gwamna Abba murna bisa lambar yabon da aka ba shi, yana mai fatan cewa za ta kara masa kwarin gwiwa wajen sauke nauyin da ke kansa.
Malam Sa'idu ya ce:
"Wannan ziyara ta kara nuna alakar da ke tsakanin mai girma gwamna da jagoranmu. Irin wannan girmamawa ne wasu da ba su kaunar ci gaba Kano ba su son gani.
"Gwamna Abba dan mutunci ne kuma ya san halacci, ba zai taba sauka daga hanyar da maigida ya dora shi a kai ba. Ina taya mai girma gwamna murna da fatan zai nunka ayyukan alhrin da yake yi."
Kwankwaso ya koka kan matsalar tsaro
A wani labarin, kun ji cewa jagoran NNPP na kasa, Rabiu Musa Kwankwaso ya nuna damuwa kan yadda tsaro ke kara tabarbarewa a sassan kasar nan.

Kara karanta wannan
Gwamnan Sokoto ya raka takwaransa na Abia ziyartar Nnamdi Kanu? An ji gaskiyar zance
Kwankwaso, tsohon ministan tsaro, ya koka kan yadda al’amuran ‘yan daba, ta’addanci, rigingimun kabilanci da yaduwar makamai ke ci gaba da zama barazana a Najeriya.
Ya ce alamar da ke nuna cewa gwamnati ta gaza, ita ce yadda take barin jihohi su rika kafa kungiyoyin 'yan sa-kai ba tare da cikakken horo ba.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Asali: Legit.ng

