'Yan Bindiga Sun Nuna Rashin Imani kan Liman da Masu Sallah a Sakkwato? An Samu Bayanai

'Yan Bindiga Sun Nuna Rashin Imani kan Liman da Masu Sallah a Sakkwato? An Samu Bayanai

  • Rahoton da ake yadawa cewa 'yan bindiga sun kai farmaki wani masallaci a karamar hukumar Sabon Birni, jihar Sakkwato ba gaskiya ba ne
  • Shugaban karamar hukumar Sabon Birni, Alhaji Ayuba Hashimu ya ce babu wani hari da aka kai masallaci har aka kashe liman
  • Sai dai mazauna kauyen Gatawa sun tabbatar da cewa yan bindiga sun kai hari tare da kashe mutane biyar da sace wasu da dama

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sokoto, Nigeria - Wasu rahotanni da aka fara yadawa sun yi ikirarin cewa 'yan bindiga sun kai mummunan hari kan musulmai a masallaci a jihar Sakkwato.

Rahoton ya nuna cewa maharan sun kashe limamin masallacin da wasu masallata a yankin karamar hukumar Sabon Birni.

Jihar Sokoto.
Taswirar jihar Sakkwato da ke Arewacin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Dagaske an kai hari masallacin Sabon Birni?

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa shugaban karamar hukumar Sabon Birni, Alhaji Ayuba Hashimu, ya yi watsi da wannan labarin, yana mai cewa ba gaskiya ba ne.

Kara karanta wannan

Liman da masallata sun rasa ransu bayan harin 'yan bindiga ana sallar asuba

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wasu kafafen yada labarai na yanzar gizo sun rawaito cewa ’yan bindiga sun shiga masallaci a Sabon Birni inda suka kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu amma shugaban karamar hukumar ya ce labarin ba shi da tushe.

A wata tattaunawa ta waya, Hon. Ayuba Hashimu ya ce:

“Ban san wani masallaci da aka kai wa hari ba, balle har a ce an kashe Liman da masallata. Labarin ƙarya ne gaba ɗaya.”

Dan Majalisar Wakilai ma ya musanta

Haka zalika, wani dan majalisa daga yankin, Hon. Aminu Boza, ya tabbatar cewa babu wani harin masallaci da ya faru a ranar Asabar.

“Ban san daga inda suka samo labarin ba, amma ba gaskiya ba ne. Babu wani masallaci da aka kai wa hari,” in ji shi.

Sai dai a wani harin daban da ya faru da safiyar yau Lahadi a kauyen Gatawa, cikin wannan karamar hukuma ta Sabon Birni, mutane biyar sun rasa rayukansu sannan mutum ɗaya ya ji munanan raunuka.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu ya 'wawure' Naira biliyan 16.5 na gyaran gadar Arewa? Gaskiya ta fito

Yan bindiga sun kashe mutum 5

Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya ce maharan sun shiga garin da tsakar dare, misalin karfe 1:30 na dare, kuma daga zuwa suka bude wuta kan mai uwa da wabi.

"’Yan bindigar sun kai hari kauyen da misalin 1:30 na dare, suka fara harbe-harbe ba kakkautawa.’Yan sa-kai sun yi kokarin tarbarsu, aka yi musayar wuta da su.
"’Yan sa-kai hudu sun mutu nan take, biyu sun ji raunin harbin bindiga aka kai su asibiti, amma ɗayansu daga baya ya rasu,” in ji shi.

Ya ce ’yan bindigar sun yi garkuwa da mutane shida, ciki har da matan aure biyu, ’yan mata biyu, da yara maza biyu, sannan sun tafi da dabbobin jama'a, in ji Leadership.

Gwamma Ahmad Aliyu.
Gwamna Ahmad Aliyu na jihar Sakkwato a gidan gwamnati Hoto: Ahmed Aliyu
Source: Facebook

'Yan bindiga sun yi barazana a Sokoto

A wani rahoton, kun ji cewa mazauna kauyuka fiye da 12 da ke yankin karamar hukumar Yabo a jihar Sakkwato sun shiga tashin hankali da zaman dar-dar.

Kara karanta wannan

'Abin da ka shuka': Kotu ta yanke wa matashi hukuncin kisa ta hanyar rataya

'Yan bindiga sun jefa mutanen wadannan garuruwa cikin tashin hankali da fargaba bayan turo wani sako da ke barazanar kawo masu farmakin rashin imani.

Barazanar 'yan bindigan na zuwa ne a daidai lokacin da matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a Arewa, musamman bayan hare-haren da aka kai jihohin Kebbi, Kwara da Neja.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262