Najeriya Ta Janye Jirgin Yakinta zuwa Benin zayan Sanin Halin da Ake Ciki

Najeriya Ta Janye Jirgin Yakinta zuwa Benin zayan Sanin Halin da Ake Ciki

  • Kasar Najeriya ta sake tunani bayan tura jirgin yakinta da ke shawagi a Jamhuriyar Benin da aka ce an yi juyin mulki
  • Najeriya ta janye jiragen yaƙinta ne daga kasar bayan hukumomi sun tabbatar da cewa komai ya lafa
  • Sojoji masu biyayya ga Shugaba Patrice Talon sun ce sun kwace birnin Cotonou da kafafen yada labarai

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ikeja, Lagos - Majiyoyi sun tabbatar da cewa kasar Najeriya ta janye jirgin yaƙin da ta tura Jamhuriyar Benin.

Hakan ya biyo bayan rahotanni da ke cewa matsalar tsaron da ta taso a kasar ta lafa, bayan yunkurin juyin mulki da aka yi.

Najeriya ta janye jirgin yakinta a Benin
Shugaba Patrice Talon na Jamhuriyar Benin. Hoto: Patrice Talon.
Source: Facebook

Najeriya ta dawo da jirginta daga Benin

Rahoton Zagazola Makama ya ruwaito cewa an yi yunkurin juyin mulki a yau Lahadi 7 ga watan Nuwambar 2025.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa ta fadi halin da ake ciki bayan yunkurin juyin mulki a Benin

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyoyin tsaro sun shaida wa cewa jirgin, wanda aka tura daga Lagos don sintiri da sa ido a yankin, an umarce shi da ya koma sansani bayan samun bayanai.

Bayanan sun nuna cewa an shawo kan lamarin kuma “ba a ga wani barazana ga tsaron kan iyakar Najeriya ba.”

A rahotannin, an ce an murkushe yunkurin juyin mulki da wasu sojoji suka yi wa gwamnatin Shugaba Patrice Talon inda dakarun gwamnati masu biyayya suka kwato cikakken iko.

Najeriya ta dawo da jirginta da ta tura Benin
Bola Tinubu da shugaban Benin, Patrice Talon. Hoto: Bayo Onanuga, Patrice Talon.
Source: Facebook

Yadda aka yi yunkurin juyin mulki

Rikicin ya fara ne bayan wasu sojojin da suka yi kaurin suna a cikin kayan soja suka ƙaddamar da farmaki domin hambarar da gwamnati.

An yi ƙoƙarin kutsa wa fadar shugaban kasa da ke Cotonou, amma dakarun gwamnati suka dakile harin.

Bayan haka ’yan tawayen sun mamaye gidan talabijin na gwamnati ORTB, inda suka kwace ikon watsa shirye-shirye.

Rundunar tsaro ta National Guard da sauran sojoji masu biyayya sun kewaye shalkwatar talabijin ɗin, suka killace ’yan tawayen.

Kara karanta wannan

Ya matso kusa da Najeriya: Sojoji sun sake juyin mulki a Afrika ta Yamma

Daga bisani, gwamnati ta tabbatar da iko a wuraren gwamnati masu mahimmanci kuma ta kwantar da tarzoma a birnin.

“Matsalar tana ƙarƙashin iko. National Guard ta mamaye komai.”

- In ji wani jami’in tsaro

Rahotannin kafafen yada labarai na cikin gida, sun nuna cewa ’yan tawayen har yanzu suna cikin gidan talabijin suna tsare, yayin da ake tattaunawa don su mika wuya ba tare da tashin hankali ba.

Babu rahoton tashin hankali ko mace-mace a titunan Cotonou, duk da cewa an bayyana birnin da tashin hankali bayan farkon rikicin.

Ana sa ran gwamnatin Benin za ta fitar da cikakken bayani kan lamarin, ciki har da sunayen ’yan tawayen da yadda yunkurin ya gaza.

An tsare Sylva kan zargin juyin mulki

Mun ba ku labarin cewa sababbin bayanai sun kara bulla a kan yadda aka alakanta tsohon Ministan man fetur, Timipre Sylva da kokarin juyin mulki.

Rahotanni sun ce hukumomin tsaro a kasar nan da suka hada da DIA, tare da EFCC da NFIU ne suka gano kudin da aka so amfani da su.

Kara karanta wannan

Yadda Yerima ya yi aure da abubuwan da suka faru bayan rigima da Wike

Kuma bayanai daga sojojin da ke hannun hukumomi sun alakanta tsohon gwamnan Jihar Bayelsa, Sylva da yunkurin kifar da gwamnati.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.