Dubun Masu Garkuwa da Mutane Ta Cika: An Cafke Hatsabiban 'Yan Bindiga a Zamfara

Dubun Masu Garkuwa da Mutane Ta Cika: An Cafke Hatsabiban 'Yan Bindiga a Zamfara

  • Jami'an Scorpion Squad sun kama rikakkun masu garkuwa da mutane biyu a Zamfara, tare da kwato motoci da bindigogi
  • Rahotanni sun tabbatar da cewa wadanda ake zargin sun sha shiga hannun hukuma, saboda yawan sace mutane da suke yi
  • An ji yadda wadannan 'yan ta'adda suka taba sace wani mutumi a Abuja, suka kwashe rabin miliyan daga asusun bankinsa

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Zamfara - Rundunar 'yan sanda ta musamman, watau Scorpion Squad ta yi nasarar cafke wasu hatsabiban masu garkuwa da mutane a jihar Zamfara.

Jami'an 'yan sandan sun cafke miyagun ne a ranar 25 ga Nuwamba 2025, bayan samun sahihan bayanan sirri da aka gudanar ta hanyar amfani da fasahar bincike ta zamani.

Rundunar 'yan sanda ta cafke masu garkuwa da mutane a Zamfara
Jami'an rundunar 'yan sanda na gudanar da bincike a kan titi. Hoto: @PoliceNG
Source: Twitter

Mai sharhi kan al'amuran tsaro a Arewacin Najeriya da kuma Tafkin Chadi, Zagazola Makama ne ya rahoto nasarar 'yan sandan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

Sojoji sun yi musayar wuta da 'yan ta'adda a Kano, an nemi wasu mutane an rasa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An cafke masu garkuwa da mutane a Zamfara

Rahoto ya nuna cewa masu garkuwar da aka kama su ne Dalhatu Bashiru, wanda aka fi sani da Yellow, mai shekaru 38, da Chidiebere Nwadigo Emmanuel, mai shekara 34.

An ce dukkan mutanen biyun tsofaffin fursunoni ne, kuma suna cikin jerin wadanda ake nema kan ayyukan garkuwa da mutane da sace motocin alfarma a jihohi daban-daban.

A yayin samamen, jami’an Scorpion Squad sun kwato mota kirar Toyota Corolla mai lambar JUX 578 AA, farar Toyota Corolla JUX 890 AA, da Toyota Camry Pencil Light mai lambar APR 459 AE.

Yadda miyagun suka sace wani mutum a Abuja

Bincike ya gano cewa an taba kama waɗannan ake zargi a Nuwambar 2023 bisa irin wannan laifi, kuma an gurfanar da su a kotu. Sai dai bayan samun beli, sun koma gidan jiya.

Bisa bayanan da suka fito daga jami’an tsaro, wadanda ake zargin sun tabbatar da cewa sun yi garkuwa da wani Segun Akinwumi O a ranar 18 ga Janairu 2024 a kusa da otel din Rita Lori da ke Garki, Abuja.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi awon gaba da amarya da sauran 'yan biki a Sokoto

Sun ce sun shiga gidansa ne suka yi awon gaba da shi zuwa hanyar Kano, inda suka tsaya a Kaduna suka karɓi katin ATM ɗinsa sannan suka cire ₦500,000 daga asusunsa.

Sai dai bayanai sun nuna cewa karyarsu ta kare ne bayan an cafke su a wani gidan sayar da fetur da ke Kaduna yayin da jami’an tsaro suka yi musu dirar mikiya, in ji rahoton News Express.

An ce wadada aka kama sun dade sun garkuwa da mutane da satar motoci
Taswirar jihar Zamfara, inda 'yan sanda suka kama rikakkun masu garkuwa da mutane. Hoto: Legit.ng
Source: Original

An gano bindigogi daga hannun 'yan ta'addan

A wancan lokacin, mutane uku daga cikin su sun tsere, amma an kama Chidiebere, Dalhatu (Yellow), daga bisani aka sake ganin suna fashi, har aka sake kama su yanzu.

A yanzu da aka kama su, jami’an tsaro sun gano bindigogi uku kirar Beretta, wadanda ake zargin suna amfani da su wajen garkuwa da mutane.

Hukumomin tsaro sun tabbatar da cewa wadanda ake zargin sun amsa cewa sun taba sace motoci sama da 20 irin SUV a Abuja cikin shekaru biyun da suka gabata.

A halin yanzu suna ci gaba da bincike da kokarin kamo sauran abokan aikinsu da suka tsere.

An cafke jagoran 'yan bindiga a Zamfara

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun sake kai hari a Kano, sun yi kisa da sace mutane

A wani labarin, mun ruwaito cewa, ’yan sanda sun kama jagoran ’yan bindiga Muhammadu Kan Kani (Akki), daga ƙaramar hukumar Bungudu, Zamfara.

An samu nasarar cafke hatsabibin dan bindigar ne a hanyar Kano zuwa Yankara (da ke jihar Katsina) bayan samun sahihan bayanan sirri.

Muhammadu Kan Kani (Akki) ya amsa cewa yana jagorantar ’yan bindigan da ke addabar garuruwan Tsafe, Yandoto da Yanwaren Daji a Zamfara.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com