Matakin Tinubu Ya Rikita Ƴan Siyasa, Sun Bazama Neman Masu Gadinsu Ta Kowane Hali
- Bayan umarnin shugaban kasa na janye jami’an ’yan sanda daga manyan mutane, an fara samun matsala game da tsaron yan siyasa
- Fitattun mutane sun fara neman jami'an tsaro daga jami'an hukumar NSCDC, gandurobobi da kamfanoni masu zaman kansu
- Rahotanni sun nuna cewa buƙatar ma’aikatan NSCDC ta karu ƙwarai, yayin da jihohi kamar Ondo ke ƙara ɗaukar Amotekun domin ƙarfafa tsaro
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Shugaban kasa Bola Tinubu ya umarci janye jami’an ’yan sanda daga manyan mutane a Najeriya domin tsaurara tsaro.
Yan siyasa sun fara buƙatar kamfanoni tsaro masu zaman kansu da NSCDC domin tsaron lafiyarsu.

Source: Facebook
Rahoton Punch ya ce Tinubu ya ba da wannan umarni domin ƙarfafa tsaro a al’umma, musamman inda ake fuskantar barazanar rashin tsaro.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
'Yan sanda sun janye masu gadin manya
Sufeta-janar na yan sanda, Kayode Egbetokun ya bayyana cewa an riga an janye jami’an tsaron da suka kai 11,566 daga manyan domin mayar da su kan ayyukan tsaron jama’a.
Binciken manema labarai ya nuna cewa yan siyasa da dama sun fara neman karin jami’an NSCDC domin kiyaye gidajensu, iyalansu, da jigilar su.
NSCDC mai ma’aikata kusan 60,000 na kare rayuka, tsare kadarorin gwamnati, da taimakawa hukumomin farar hula.
A Abuja, an ce jami’an NSCDC na samun kira da saƙonni daga manyan mutane masu neman sababbin masu tsaro, duk da ƙarancin ma’aikata a halin yanzu.
Jihohi kamar Ondo sun fara ɗaukar matakan tallafawa tsaro, inda Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya amince da ɗaukar ma’aikatan Amotekun 500 domin ƙarfafa kariya.
A taron gwamnonin Kudu, an jaddada cewa babu makawa sai an kafa ’yan sandan jihohi idan ana son magance matsalar ’yan bindiga yadda ya kamata.

Kara karanta wannan
Abu ya gagara: Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan matsalar tsaron Najeriya

Source: Facebook
Yadda yan siyasa ke neman jami'an kariya
Wasu kamfanonin tsaro masu zaman kansu ma sun ce sun kasa biyan bukatar manya saboda ƙarancin ma’aikata da ƙaruwar buƙatar tsaro a lokaci guda.
Wasu ’yan siyasa sun killace kansu a gidajensu har sai sun samu sababbin tsare-tsare, suna ganin matakin ya dace da halin tsaro na yanzu, cewar The Nation.
Sanata Ali Ndume ya yaba da umarnin, yana mai cewa ya kamata a rage yawan ’yan sandan da ke aiki da ’yan majalisa domin mayar da su ga jama’a.
Ya ce abin kunya ne yadda manya ke amfani da jami’an tsaro da yawa, har ma a kan matansu da ’ya’yansu, yayin da talakawa ke rasa kariya.
Janye 'yan sanda: An fara cika umarnin Tinubu
Mun ba ku labarin cewa Rundunar 'yan sandan Najeriya ta fara cika umarnin da Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayar a kan jami'anta.
Shugaba Tinubu ya yi umarnin a janye dukkanin jami'an 'yan sanda da ke tsaron manyan mutane a fadin Najeriya.

Kara karanta wannan
Yadda 'Yan sanda suka saba alkawarin janye jami'ai daga gadin manya amma ba a cikawa
Bola Tinubu ya bayar da umarnin bayan an samu karuwar hare-hare, musamman a makarantun da ke karkara a kasar.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
