Kungiyar CAN Ta Yi Magana bayan Sace Dalibai a Niger, Ta ba Kiristoci Shawara

Kungiyar CAN Ta Yi Magana bayan Sace Dalibai a Niger, Ta ba Kiristoci Shawara

  • Kungiyar Kiristoci ta Najeriya reshen Niger ta yi magana game da harin da yan bindiga suka kai a daya daga cikin makarantun Kiristoci
  • CAN ta la’anci harin da ‘yan bindiga suka kai St. Mary’s Papiri, inda aka sace dalibai, malamai da ma’aikacin tsaro
  • Kungiyar ta ce harin ya faru tsakanin ƙarfe 1:00 zuwa 3:00 na dare, inda ‘yan ta’adda suka shiga makarantar, suka harbi mai gadi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Minna, Niger - Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen Niger ta yi martani kan sace dalibai da malamai a jihar.

Kungiyar ta yi Allah-wadai da harin da ‘yan bindiga suka kai makarantar St. Mary’s da ke Papiri a jihar wanda ya yi sanadin sace dalibai.

Yan bindiga sun sace dalibai a Niger
Taswirar jihar Niger wacce ke cikin jihohin da ke dama da rashin tsaro. Hoto: Legit.
Source: Original

Niger: CAN ta yi Allah-wadai da sace dalibai

Kara karanta wannan

Sace dalibai: Atiku da Kwankwaso sun fadawa Tinubu matakan da ya kamata ya dauka

A wata sanarwa da shugaban kungiyar ya fitar wanda Channels TV ta samu, shugaban Rabaran Bulus Yohanna ya bayyana takaici kan harin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yohanna ya bayyana cewa harin ya hada da sace wasu malamai da ma’aikatan tsaro da aka dauke da ƙarfi.

Ya kara da cewa lamarin ya faru ne tsakanin ƙarfe 1:00 na dare zuwa 3:00 na dare, ranar Juma’a.

Sanarwar ta ce:

“Shugaban CAN na jihar Niger Rabaran Bulus Dauwa Yohanna, yana sanar da cewa wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun mamaye St. Mary da ke Papiri, karamar hukumar Agwarra a jihar Niger.
“Lamarin ya faru ne tsakanin ƙarfe 1:00 zuwa 3:00 na daren Juma’a, 21 ga Nuwamba 2025, inda suka yi garkuwa da dalibai, malamai da kuma wani ma’aikacin tsaro da suka harbe.
“CAN ta yi tir da wannan mummunan hari tare da nuna damuwa kan lafiyar yaran da aka sace da iyalansu."

Yohanna ya tabbatar wa jama’a cewa cocin na aiki tare da jami’an tsaro, shugabannin al’umma da hukumomin gwamnati domin ceto wadanda aka sace.

Kara karanta wannan

Cocin katolika ya fadi halin da ake ciki bayan sace dalibai a Neja

CAN ta yi Allah-wadai bayan sace ɗalibai a Niger
Shugaban kungiyar CAN a Nigeria, Rabaran Bulus Yohanna. Hoto: Catholic Broadcast Commission, Nigeria.
Source: Facebook

Rokon da CAN a Niger ta yi ga al'umma

Shugaban, wanda shi ma Fasto ne a cocin Kontagora ya roki jama’a da su kwantar da hankali, su taimaka wa hukumomi, tare da ci gaba da addu’a domin dawo da yaran cikin koshin lafiya.

“CAN na nan daram wajen kare ‘ya’yanmu, kuma za ta rika sanar da karin bayani idan an samu tabbacin sahihancin rahotanni.
“Mu roki Ubangiji ya kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su, kuma ya ci gaba da kiyaye jama’arsa daga dukkan hadurra.”

- Kungiyar CAN

Rahotanni sun ce maharan sun kutsa makarantar ne a yankin Agwara da sassafe inda suka yi barna, cewar rahoton Punch.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa ‘yan bindigan sun zo da yawa, kan babura fiye da 60 tare da wata mota, suka kai harin.

An ce sun harbi mai gadin makarantar, wanda yanzu haka yake dauke da munanan raunuka.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun sake shiga makaranta sun sace dalibai da malamai a Neja

Cocin Katolika ya magantu kan sace daliban Niger

Mun ba ku labarin cewa Cocin Katalika a jihar Niger ya tabbatar da harin da yan bindiga suka kai a daya daga cikin makarantun Kiristoci tare da kwashe yara da malamai.

Majiyoyi sun bayyana cewa an sace daliban a safiyar ranar Juma'a, 21 ga watan Nuwambar 2025, lamarin da ya kara gigita mazauna Arewacin Najeriya.

Harin na zuwa ne kwanaki kadan bayan sace daliabi a wata makaranta da ke jihar Kebbi, tare da kashe mataimakin shugaban makarantar.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.