Kusa a APC Ya Ji Kunya, Ya Nemi Afuwar Majalisa kan Zargin Cin Hancin N14bn
- Jigon APC ya rusuna a gaban majalisar dattawa inda ya nemi afuwa game da zargin su da karbar cin hancin
- Alwan Hassan wanda ya fito daga Kano, ya janye ikirarin cewa sanatoci sun karɓi dala miliyan 10 don jinkirta tantance Abdullahi Ramat
- Ya bayyana cewa ya dogara da maganganun da ya ji wajen bibiyar dalilin jinkirin tabbatar da Ramat a NERC
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Jigon jam'iyyar APC, Alwan Hassan ya nemi afuwa a gaban majalisa bayan zargin mambanta da karbar cin hanci.
Alwan Hassan wanda ya zargi sanatoci da karɓar dala miliyan 10 don jinkirta tabbatar da Abdullahi Ramat a shugabancin NERC, ya janye wannan kalamansa.

Source: Twitter
'Dan APC ya nemi afuwar majalisa kan sharri
Alwan Hassan wanda ɗan siyasa ne daga Kano, ya ce ya yi wannan magana ne bisa bayanan da ya ji yayin neman fahimtar dalilin da yasa Majalisar ta jinkirta tabbatarwar, cewar Premium Times.
Ya nemi afuwa ga shugabancin Majalisar Dattawa a taron manema labarai a Abuja, inda ya ce bayan bincike ya gane cewa zargin ba gaskiya ba ne.
A cewarsa, ya yi maganganun da ba su dace ba game da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Mataimakinsa Barau Jibrin, wanda yanzu ya gane kuskure ne.
Ya kara da cewa zargin da ya ambata ya fito ne daga tattaunawar da ya yi da mutane, amma daga baya ya fahimci cewa ba daidai bane ko kadan.
Alwan ya ce ya janye zargin gaba ɗaya ba tare da wata shakka ba, tare da neman afuwa ga Majalisa da shugabanninta kan duk wani rashin gaskiya da aka danganta musu.

Source: Facebook
Zargin da ake yiwa kusan na APC
Janyewarsa ta biyo bayan kama shi da kuma tsare shi da ’yan sanda suka yi kan wannan zargi, duk da cewa ba a bayyana tsawon lokacin tsarewar ba.

Kara karanta wannan
Hadimin Buhari ya karyata dan majalisar Amurka kan sace daliban Kebbi a 'yankin Kiristoci'
An ce manyan mutane sun shiga tsakani suka taimaka wajen ganin an sake shi, bayan ya shaida wa manema labarai makonni da suka gabata cewa an ba sanatoci cin hanci.
Ramat dai ya kwashe sama da wata guda yana jiran Majalisa ta tabbatar da shi, bayan Shugaba Bola Tinubu ya mika sunansa don duba cancantarsa.
Rokon da Alwan Hassan ya yi ga majalisa
Bayan neman afuwa, Hassan ya sake roƙon Majalisar Dattawa da ta amince da Ramat, yana mai jaddada cewa yana da kwarewa mai sosai ga tsarin makamashin kasa.
Ya ce yana girmama rawar da Majalisar ke takawa, kuma wannan lamari ya koya masa muhimmancin bin ka’ida da mutunta cibiyoyin dimokiradiyya.
Matashin ya ce yana da kishin gaskiya, amma hakan ya koya masa cewa ya kamata duk wani yunkuri ya kasance cikin ladabi da bin doka.
An bukaci karin wata jiha a Najeriya
Kun ji cewa kungiyar Aba State Movement (ASM) ta bukaci majalisar dokoki ta tabbatar da Aba a matsayin jiha ta shida a Kudu maso Gabas.
Ta ce an dade ana gabatar da bukatar ga majalisar kasa tun daga 1952, tare da cewa Aba ta cika dukkan sharudda a tsarin mulki.
Shugaban kungiyar ya kara da cewa Ohanaeze Ndigbo ta nuna goyon bayan mayar da Aba zuwa jiha ta shida a yankin.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

