Bayan Ficewar 'Yan Majalisa, Shugaban PDP a Taraba Ya Yi Murabus daga Jam'iyyar

Bayan Ficewar 'Yan Majalisa, Shugaban PDP a Taraba Ya Yi Murabus daga Jam'iyyar

  • Jam'iyyar PDP mai mulki a jihar Taraba ta sake samun koma bayan murabus din shugabanta daga kan mukaminsa
  • Alhaji Abubakar Bawa ya yi murabus daga mukaminsa tare da ficewa daga jam'iyyar PDP ba tare da bata lokaci ba
  • Shugaban na PDP ya bayyana cewa rikice-rikicen da suka addabi jam'iyyar na daga cikin dalilan sa suka sanya ya raba gari da ita

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Taraba - Shugaban jam’iyyar PDP na jihar Taraba, Alhaji Abubakar Bawa, ya yi murabus daga kan mukaminsa.

Hakazalika, shugaban na PDP ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar mai mulki a jihar Taraba.

Shugaban PDP a Taraba ya yi murabus
Alhaji Abubakar Bawa a cikin ofis Hoto: @AdamuWaziri
Source: Twitter

Tashar Channels tv ta kawo rahoton cewa Alhaji Abubakar Bawa ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a ranar Litinin, 17 ga watan Nuwamban 2025.

Kara karanta wannan

Abu ya kacame, sabon shugaban PDP da tsagin Wike na iya arangama a taro

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa shugaban PDP ya fice daga jam'iyyar?

Alhaji Abubakar Bawa ya ce shawarar da ya yanke ta biyo bayan rikicin shugabanci da kuma shari’o’in da suka dabaibaye jam’iyyar PDP a matakin kasa.

“Ina so na sanar da ku da ma jama’ar Taraba cewa na yi murabus daga kasancewa mamba a jam’iyyar PDP, kuma na riga na rubuta wa shugaban gundumata takardar murabus.”
“Takardata na cewa: Ina sanar da ficewata daga jam’iyyar PDP tun daga 17 ga watan Nuwamba, 2025.”

- Alhaji Abubakar Bawa

Bawa ya bayyana cewa matakin nasa ya kasance ne bayan dogon tunani da nazarin rikice-rikicen da suka addabi jam’iyyar a matakin kasa, musamman rikicin shugabanci mai tsawo da shari’o’in da suka janyo rashin tabbas a tsarin PDP.

“Rikicin shugabanci da shari’o’in da suka daɗe suna faruwa sun haifar da rashin tsari, wanda ya sa ya zama da wuya na ci gaba da bin tafiyar jam’iyyar cikin wannan hali.”

Kara karanta wannan

Makarfi: Tsohon gwamnan Kaduna ya ajiye mukaminsa a PDP, ya fadi dalilin murabus

- Alhaji Abubakar Bawa

Bawa ya hidimtawa PDP a Taraba

Jaridar Leadership ta ce ya bayyana cewa ya yi aikin jam’iyyar da gaskiya da amana tsawon shekaru, musamman a matsayinsa na shugaban PDP na jihar Taraba, yana mai gode wa jami’an jam’iyyar bisa amincewa da goyon baya da suka ba shi.

Shugaban PDP a Taraba ya yi murabus
Alhaji Abubakar Bawa wanda ya shugabanci PDP a jihar Taraba Hoto: @AdamuWaziri
Source: Twitter

Bawa ya ce tafiyarsa a PDP ta kasance ta hidima, sadaukarwa da jajircewa ga dimokuradiyya, amma saboda kare mutuncinsa da ka’idojinsa, ya ga dacewa ya koma gefe domin tantance makomar siyasarsa.

A karshe, ya gode wa shugabannin jam'iyyar da mambobi bisa haɗin kai da zumunci da suka nuna masa a lokacin da yake jagoranci.

Shugaban majalisa ya fice daga PDP

A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban majalisar dokokin jihar Taraba, ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar PDP mai mulki a jihar.

Rt Hon. Kizito Bonzena, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar PDP zuwa APC mai mulkin kasar nan tare da sauran mambobi 15 na majalisar dokokin jihar.

Kara karanta wannan

Sule lamido ya fadi matsayarsa kan taron PDP da ya nemi kotu ta dakatar

Shugaban majalisar dokokin ta Taraba ya bayyana cewa ya fice daga PDP zuwa jam'iyyar APC ba don wata manufa ta kashin kansa ba, sai don maslahar jihar Taraba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng