Babbar Magana: An Kashe Mataimakin Shugaban APC, 'Yan Sanda Sun Dauki Mataki

Babbar Magana: An Kashe Mataimakin Shugaban APC, 'Yan Sanda Sun Dauki Mataki

  • Rundunar 'yan sanda ta tabbatar da kisan mataimakin shugaban APC na karamar hukumar Ethiope ta Gabas a jihar Delta, Ese Idisi
  • Rahoto ya nuna cewa wasu mahara ne suka kashe jigon jam'iyyar APC yayin da suka kai hari kauyen Okpara ranar Asabar da ta gabata
  • Jam'iyyar APC reshen jihar Delta ta yi Allah wadai da lamarin, ta kuma bukaci jami'an tsaro su binciko duk wani mai hannu a kisan

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Delta, Nigeria - Wasu mahara da ba a san ko su waye ba sun hallaka mataimakin shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Ethiope ta Gabas a jihar Delta, Mista Ese Idisi.

Rahoto ya nuna cewa maharan sun hallaka babban jigon APC ne a lokacin da suka farmake shi a jihar Delta da ke Kudancin Najeriya ranar Asabar da ta gabata.

Kara karanta wannan

Naira tiriliyan 1.4 sun yi ƙafa a CBN, an taso gwamnan babban banki ya yi bayani

Yan sandan Najeriya.
Hoton wasu jami'an yan sanda a bakin aiki Hoto: @PoliceNG
Source: Twitter

Matakin da 'yan sanda suka dauka

Jaridar Punch ta tattaro cewa rundunar yan sanda reshen jihar Delta ta tabbatar da kisan Mista Idisi a wata sanarwa da jami'in hulda da jama'a, SP Bright Edafe ya fitar yau Litinin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce duk da cewa duk da babu cikakkun bayanai a yanzu, amma rundunar ta samu tabbacin kashe Idisi a Okpara, wani kauye da ke cikin karamar hukumar.

SP Edafe ya ce:

“Mun karɓi rahoton cewa an kashe shi, kuma yanzu haka mun fara gudanar da bincike.”

APC ta yi Allah-wadai da kisan

APC ta jihar Delta ta bayyana alhini da takaicin wannan kisa mai muni, tana mai Allah-wadai da lamarin a wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na jam’iyyar, Mr. Valentine Onojeghuo, ya fitar.

A sanarwar, jam’iyyar APC ta bukaci ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su gudanar da bincike mai zurfi, ba tare da son rai ba don gano wadanda suka aikata wannan danyen aiki.

Kara karanta wannan

Ga wata sabuwa: Manyan 'yan siyasa 3 sun maka shugaban jam'iyyar APC a kotu

Haka kuma, APC ta nemi a binciko wadanda suka dauki nauyi, da duk wanda ke da hannu a wannan aika-aika, "Dole ne a kamo su tare da gurfanar da su a gaban shari’a ba tare da bata lokaci ba.”

Jam'iyyar APC.
Hoton tutar jam'iyyar APC mai mulki Hoto: OfficialAPCNig
Source: Twitter

APC ta mika sakon ta'aziyya

Jam’iyyar ta mika ta’aziyyarta ga iyalan mamacin, tana mai cewa rashin Idisi babban gibi ne ga iyalinsa, al’umma, da kuma jam’iyyar APC musamman a mazabar Ethiope ta Gabas 4.

Ta bayyana shi a matsayin mamba nagari, mai biyayya, jajirtacce kuma abin dogaro wanda ya bayar da gudummawa sosai ga cigaban jam’iyyar APC a Ethiope ta Gabas.

"Rasuwarsa ba kawai rashin jigo ba ce, babban rauni ne da ya jefa mu cikin baƙin ciki," in ji APC.

Mahara sun harbe 'dan APC a Zamfara

A wani rahoton, kun ji cewa 'yan bindiga sun kashe jigon APC a jihar Zamfara, Hon. Umar S. Fada Moriki a kan hanyar Tsafe.

Marigayin ya shahara wajen kokarin kamanta gaskiya a ayyukansa, musamman kokarinsa na ganin yankin Shinkafi da Zurmi sun samu ci gaba cikin kwanciyar hankali.

Wannan na zuwa ne yayin da rashin tsaro da ake fama da shi a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya na ci gaba da ta'azzara.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262