Shugaban Najeriya Ya Shiga Cikin Jerin Mukaman Siyasa 20 Mafi Ƙarfi a Duniya

Shugaban Najeriya Ya Shiga Cikin Jerin Mukaman Siyasa 20 Mafi Ƙarfi a Duniya

  • Kujerar shugaban kasa a Najeriya ta shiga jerin manyan mukaman siyasa 20 mafi karfi da tasiri a bangarori daban-daban a duniya
  • A wani rahoton kididdiga, an tattaro mukamai mafi karfi a duniya ciki har da shugabannin kasashe irinsu Amurka, China da kasar Rasha
  • Kasashe masu tasowa kamar Najeriya sun shiga wannan jeri ne saboda rawar da suke takawa wajen samar da tsaro da inganta tattalin arziki a yankunansu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Wani sabon rahoton ƙididdiga na duniya ya fitar da jerin manyan mukaman siyasa 20 masu tasiri fiye da kowane a halin da ake ciki yanzu a doron kasa.

Ana ganin wadannan mukamai guda 20, su na karfin fada a ji wajen inganta harkokin tsaro, karfin tattalin arziki da al'amuran diflomasiyya a tsakanin kasa da kasa.

Shugaban Amurka, Donald Trump.
Hoton shugaban Amurka, Donald Trump yana jawabi a taro Hoto: Getty Images
Source: Twitter

Amurka da Rasha sun shiga ciki

Kara karanta wannan

'Yan majalisar dokoki sun tsawaita wa'adin shugaban kasa a Benin

Jaridar The Nation ta tattaro cewa jerin ya haɗa shugabannin manyan ƙasashe irin su Amurka, China, India, Jamus, da Rasha, wadanda ake ganin sun fi karfi a duniya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Haka zalika wadannan mukamai sun nuna karuwar tasirin ƙasashe masu tasowa kamar Brazil, Indonesia, da kuma Najeriya.

Haka kuma, rahoton ya sanya Tarayyar Turai (EU) a jerin, alamar cewa ikon ƙungiyar ƙasashe yana ƙaruwa sosai a wannan zamani na haɗin kai.

Jerin mukamai 20 mafi karfi a duniya

Ga jerin manyan mukaman siyasa 20 mafi ƙarfi a duniya:

1. Shugaban kasar Amurka

2. Sakataren Janar na Jam’iyyar Kwaminis ta China

3. Firaminiatan kasar India

4. Shugaban Hukumar Tarayyar Turai (EU)

5. Kansilan Jamus

6. Shugaban kasar Rasha

7. Firaministan kasar Birtaniya

8. Shugaban kasar Faransa

9. Firaministan kasar Japan

10. Sarkin kasar Saudiyya

11. Shugaban kasar Turkiyya

12. Firaministan kasar yahudaa watau Isra’ila

13. Firaministan kasar Kanada

14. Shugaban kasar Brazil

15. Magajin Garin birnin New York City da ke kasar Amurka

16. Shugaban Koriya ta Kudu

17. Shugaban kasar Indonesia

18. Firaministan kasar Italiya

19. Shugaban kasar Mexico

Kara karanta wannan

'Sai mun biya': Al'umma sun fadi makudan kudi da suke ba 'yan bindiga domin kariya

20. Shugaban kasar Najeriya

Me yasa Najeriya ta shiga jerin?

Rahoton ya bayyana cewa matsayi na 20 da Shugaban Najeriya ya samu ya samo asali ne daga abubuwa da dama ciki har da girman tattalin arzikin Najeriya a nahiyar Afirka.

Shugaba Bola Tinubu.
Hoton shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu Hoto: @OfficialABAT
Source: Twitter

Sauran dalilan da aka duba wajen sanya Najeriya a matsayi na 20 akaai tasirinta a diflomasiyyar yanki musamman a ECOWAS da rawar da take takawa a tsaro da yaki da ta’addanci a yankin Sahel

Bugu da kari, an ruwaito cewa yawan al’ummar Najeriya da ke da matsayi na 6 mafi yawa a duniya, ya taka muhimmiyar rawa.

Majalisa ta kara wa'adin shugaban Benin

A wani labarin, kun ji cewa majalisar dokokin Jamhuriyar Benin da ke Yammacin Afirka ta tsawaita wa'adin shugaban kasa zuwa shekaru bakwai.

Sabuwar dokar ta ayyana cewa shugaban ƙasa a Jamhuriyar Benin zai yi mulki na shekaru 7 kacal, kuma ana iya sabunta shi sau ɗaya tak.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi garkuwa da dan kasuwa kuma tsohon shugaban jam'iyyar PDP

Wannan gyara na zuwa ne kafin zaben shugaban kasa da za a yi a 2026 a jamhuriyar Benin, kasar da ke magana da harshen Faransanci a Yammacin Afirka.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262