Tsohon Hafsan Tsaro, Irabor Ya Tsoma Baki kan Rigimar Wike da Matashin Soja a Abuja

Tsohon Hafsan Tsaro, Irabor Ya Tsoma Baki kan Rigimar Wike da Matashin Soja a Abuja

  • Janar Lucky Irabor (mai ritaya) ya nuna damuwa kan halayyar da ministan Abuja, Nyesom Wike ya nuna a takaddamarsa da sojan ruwa
  • Tsohon babban hafsan tsaron Najeriya (CDS) ya ce kalmomin da Wike ya yi amfani da su sun yi daci, musamman ga wanda ke sanye da kakin soja
  • Irabor, wanda ya jagoranci sojojin Najeriya a mulkin Buhari, ya bukaci a girmama kakin soja saboda yana wakiltar karfin ikon kasa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Tsohon Babban Hafsan Tsaro na Ƙasa (CDS), Janar Lucky Irabor (mai ritaya) ya yi tsokaci kan rikicin da ya faru tsakanin ministan Abuja, Nyesom Wike da matashin sojan ruwa.

Idan baku manta ba, Wike ya yi cacar baki har da amfani da kalamai masu zafi a rigimar da ta faru tsakaninsa da Laftanal A. M Yerima a wani fili a Abuja ranar Talata.

Kara karanta wannan

ADC ta yi mamakin matakin da Tinubu ya dauka bayan sabanin Wike da A.M Yerima

Lucky Irabor.
Hoton tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Lucky Irabor (mai ritaya) Hoto: @DHQNigeria
Source: Twitter

Jaridar The Cable ta ce yayin da yake martani, tsohon CDS ya soki yadda Wike ya yi wa matashin sojan wanda ya nanata cewa yana bin umarni daga sama.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Irabor ya yi wannan bayani ne a ranar Alhamis a Abuja, a wurin taron da kungiyar Editocin Najeriya (ANEC) karo na 21.

Kalamai masu zafi da Wike ya fada

Bidiyoyi da suka yadu sun nuna yadda sojojin ruwa suka hana ministan shiga wani filin da ake takaddama a kai, lamarin da ya haifar da musayar yau zafi.

A lokacin da takaddama ta barke a tsakaninsu, Wike ya kira sojan ruwa, Laftanal AM Yerima, da kalmar “wawa”.

Da yake mayar da martani kan lamarin, tsohon CDS, Irabor ya ce babban abin dubawa shi ne kimar rigar soja da kuma rantsuwar hidimar ƙasa da ta ƙunsa.

“Kakin soja ba ruwansa da wanda ya sanya shi, wannan kaki yana wakiltar ikon kasa, ko matashi ko babba ne ya sanya kakin soja, yana wakiltar kasa ne gaba daya."

Kara karanta wannan

A.M Yerima: Tsohon jigon APC, Frank ya shawarci Tinubu ya ja kunnen Wike

Irabor ya zargi Wike da cin mutuncin soja

Irabor ya ƙara da cewa cin mutuncin soja da irin waɗannan kalamai da Wike ya yi amfani da su tamkar cin mutuncin ikon da shugaban ƙasa ya dora a kan rundunar soji ne.

Tsohon babban hafsan tsaron ya bukaci a duba wannan abu da ya faru ta hanyar amfani da dokokin gidan soja, sannan a duba niyya da kuma aiki, in ji Vanguard.

Lucky Irabor ya ce lamarin bai tsaya iya ikon da Minista ke da shi kan filaye ko zargin matashin soja ya aikata laifi ba, sai dai kalaman Wike sun keta mutuncin kasa.

Wike da A. M Yerima.
Hoton Ministan Abuja, Nyesom Wike da matashin soja, A. M Yerima a wurin da suka yi cacar baki a Abuja Hoto: Datti Assalafy
Source: Facebook

Ya yi kira ga kafafen yada labarai da su wayar da kan jama’a kan muhimmancin rantsuwar aiki da kimar kakin soja, yana mai cewa ilimin ɗabi’un ƙasa yana raguwa a Najeriya.

An bukaci Tinubu ya ja kunnen Wike

A wani labarin, kun ji cewa tsohon jagora a APC, Timi Frank ya bayyana takaici a kan rikicin Ministan Abuja, Nyesom Wike da jami'in sojan ruwa, A.M Yerima.

Kara karanta wannan

'Ka nemi kashe ni,' Wike ya yi martani mai zafi ga Buratai bayan rigima da soja

Ya bayyana lamarin a matsayin alama ta lalacewar tsarin shugabanci a Najeriya da kuma barazana ga dimokuraɗiyya a kasar nan.

Frank ya bukaci Tinubu ya ja kunnen Wike, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa tana mutunta doka, ladabi da kuma ƙoƙarin kare hukumomi.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262