Dubu Ta Cika, Sojojin Najeriya Sun Kama Mai Sayar wa Ƴan Ta'adda Makamai a Taraba

Dubu Ta Cika, Sojojin Najeriya Sun Kama Mai Sayar wa Ƴan Ta'adda Makamai a Taraba

  • Sojojin Najeriya sun cafke wani mai safarar makamai ga 'yan ta'adda a yayin samamen Operation Lafiya Nakowa a Taraba
  • Rundunar ta ce an kama Abdulmudallabi Audu, mai shekaru 25, a Shagada, Gassol, dauke da bindiga da tulin harsasai
  • Janar Kingsley Uwa ya yaba da aikin dakarun, yana mai cewa rundunar za ta ci gaba da murkushe ‘yan bindiga a kasar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Taraba - Sojojin Brigade ta 6 na rundunar sojin Najeriya da ke karkashin Operation Whirl Stroke sun samu asarar gurgunta ayyukan 'yan ta'adda a Taraba.

Rundunar sojin Brigade ta 6 ta bayyana cewa dakarunta sun kama wani mutum da ake zargin mai safarar makamai ne, kuma an same shi da bindigar AK-47 da harsasai 53.

Sojojin Najeriya sun kama wani da ake zargin yana sayarwa 'yan ta'adda makamai a Taraba
Dakarun sojojin Najeriya sun kai samame wani kauye, inda suka kama mai safarar makamai. Hoto: @ZagazOlaMakama
Source: Twitter

Jaridar Punch ta rahoto cewa sojoji sun gudanar da samamen ne a ƙarƙashin aikin Operation Lafiya Nakowa a ranar 12 ga Nuwamba, 2025, a kauyen Shagada, cikin gundumar Namnai, karamar hukumar Gassol.

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun tarwatsa yunkurin sace jami'ansu da limamin addini a Abuja

Taraba: Sojoji sun kama mai safarar makamai

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Laftanar Umar Muhammad, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar sojin Brigade ta 6, ya fitar ranar Laraba.

Laftanal Umar Muhammad ya ce sojojin sun kai samamen ne bayan samun sahihin bayanan sirri daga mazauna yankin.

Sanarwar ta ce:

“An kama wanda ake zargi, Abdulmudallabi Audu, mai shekaru 25, a lokacin da ake gudanar da samamen. An same shi da bindigar AK-47, da harsasai 53.”

A cewarsa, an kwashe wanda ake zargin tare da kayan da aka kwato zuwa hedkwatar Brigade ta 6 domin ci gaba da bincike da kuma yuwuwar gurfanar da shi gaban kuliya.

An jinjinawa dakarun da suka kai samame

Brigadier Janar Kingsley Uwa, kwamandan Brigade ta 6, ya yabawa dakarun saboda kwazo da saurin kai samamen da suka yi bayan samun bayanan sirri.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da gudanar da ayyuka na musamman domin kawar da masu laifi, masu safarar makamai, da sauran masu aikata miyagun ayyuka a Taraba.

Kara karanta wannan

Rai ya yi halinsa: Mahaifiyar minista a gwamnatin Tinubu ta rasu

Jaridar Sun ta rahoto Janar Kingsley Uwa ya nemi mazauna yankin da su ci gaba da ba da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin taimaka musu wajen kawarda ‘yan ta’adda.

Sojoji sun nemi al'ummar Taraba su ic gaba da sahihan bayanai da za su taimaka wajen kawar da 'yan ta'adda
Taswirar jihar Taraba da ke a Arewa maso Gabashin Najeriya. Hoto: Legit.ng
Source: Original

Hedkwatar soji ta tabbatar da tsaro a kasa

A wani labari mai alaka da wannan, Babban Hafsan Sojin Kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa tsaro zai inganta a makonni masu zuwa.

Jaridar The Nation ta rahoto Laftanar Janar Waidi ya bayyana hakan ne bayan ganawarsa da Shugaba Bola Tinubu a fadar Aso Rock, Abuja, inda ya ce:

“’Yan Najeriya su yi hakuri, za a ga tsaro ya inganta nan ba da jimawa a duk fadin kasar nan.”

Hafsan sojin kasan ya ce ganawarsa da Tinubu na da alaka da ayyukan sojoji da ake gudanarwa a Arewa maso Gabas da yadda za a inganta tsaro a kasar.

Zamfara: An kama mai safarar makamai

A wani labarin, mun ruwaito cewa, wata mata mai safarar makamai a jihar Zamfara ta shiga hannun jami'an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Kara karanta wannan

Ba sauki: Jiragen yakin sojojin sama sun yi ruwan wuta kan 'yan ta'adda a jihohin Arewa 3

Jami'an na hukumar NDLEA sun cafke matar ne dauke da kayan laifin wadanda ake zargin ta shirya kai su ga 'yan bindiga da ke cikin daji.

An ce matar ta fito ne daga karamar hukumar Birnin Magaji, inda aka gano harsasan a cikin kayanta lokacin da jami’an NDLEA suka dakatar da ita domin bincike.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com