‘Kun Fi Tsoron Trump Sama da Allah’: Malamin Musulunci ga Manyan Arewa

‘Kun Fi Tsoron Trump Sama da Allah’: Malamin Musulunci ga Manyan Arewa

  • Sheikh Murtala Bello Asada ya yi magana kan azzaluman shugabannin Najeriya bayan Shugaba Donald Trump ya yi barazana ga kasar
  • Malamin ya nuna takaici yadda wasu shugabanni suke tsoron Trump fiye da Allah, yana cewa hakan alamar azzalumai ne masu son duniya
  • Ya roki Allah ya rikita azzalumai da ke goyon bayan masu ta’addanci kamar Bello Turji, yana addu’a Amurka ta samu nasara kansu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Sokoto - Malamin addinin Musulunci a Najeriya, Sheikh Murtala Bello Asada ya yi magana kan rashin tsaro a Arewacin Najeriya.

Malamin ya tabo maganar barazanar Donald Trump inda ya ce azzaluman shugabanni a Najeriya sun ji kunya.

Malamin Musulunci ya soki azzalumai masu goyon bayan Turji
Sheikh Murtala Bello da dan ta'adda, Bello Turji. Hoto: Malam Murtala Bello Sokoto, NQ Nigerian Army.
Source: Facebook

Sheikh Asada ya dura kan azzaluman Najeriya

Malamin ya bayyana haka ne a cikin wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a jiya Litinin 10 ga watan Nuwambar 2025.

Kara karanta wannan

Kungiyar Musulman Najeriya ta yi tsokaci kan ikrarin Trump na yiwa Kirisoci kisan gilla

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin bidiyon, Sheikh Asada ya ce azzalumai a Najeriya suna tsoron shugaban Amurka, Donald Trump fiye da Allah mahalicci.

Ya ce:

"Kun ga miyagu azzalumai, makiya Allah hankalinsu ya tashi sun rikice, idan ba ku manta ba, shekaran jiya na fada muku azzaluman Najeriya sun fi jin tsoron Trump sama da Allah.
"Ku duba shugaban kasar Amurka ya yi magana sun rude, hankalinsu a tashi, wannan yana nuna Allah yana da abubuwan da yake rikita azzalumai.
"Allah ka kara riktia su, ka rikita azzalumai, muna rokon ka ka kawo mana zaman lafiya a kasarmu, wannan wa'azi ne sai mai hankali zai gane gaskiya."
Malam Murtala Bello ya soki azzaluman shugabanni a Najeriya
Bola Tinubu da Sheikh Murtala Bello Asada. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu, Malam Murtala Bello Sokoto.
Source: Facebook

Murtala Asada ya daura laifi kan manyan Arewa

Sheikh Murtala Bello ya ce manyan Arewa sun ji kunya saboda ba su da kishin yankinsu kamar yadda yan Kudu suka nuna suna da manya.

Ya ce ko mutum bai san me yake yi ba, ya san babu wadanda suka zalunci Musulunci da yankin Arewa face manyan yankin.

Kara karanta wannan

'Abin da Rasha, China za su yi bayan harin Amurka': Malami ya gargadi Tinubu

Ya kara da cewa:

"Ana nuna mana cewa manyan Arewa ko suna so ba su so sun ji kunya, mutanen Kudu sun nuna suna da manya.
"Sai gashi manyan Arewa sun zo suna kame-kame, wai an taso wa Musulunci, an taso muku din, yanzu hankalinku ya tashi saboda dukiyoyinku da ke kasashen waje.
"Tallafi da ake samowa daga kasashen waje shi ne tashin hankalin Najeriya, wallahi ko ka ki ko kaso mutanen Arewa su suka zalunci al'ummar Musulmin Arewacin Najeriya."

Malamin ya koka kan yadda azzalumai suka tayar da hankulansu game da barazanar Trump inda ya yi addu'ar Allah ya ba Amurka sa'a kan masu daurewa Bello Turji gindi.

Murtala Bello ya soki sulhu da Turji

A baya, an ji cewa malamin addinin musulunci, Sheikh Murtala Bello Asada, ya yi fatali da batun yin sulhu da jagoran 'yan bindiga, Bello Turji.

Sheikh Asada ya bayyana cewa ya kamata mutane su tashi su kare kansu maimakon tattauna da 'yan ta'adda marasa amana.

Kara karanta wannan

Dan majalisar Amurka ya kuma jan kunnen Tinubu kan wasa da barazanar Trump

Hakazalika ya kuma karyata wani faifan murya da ake yadawa yana tattaunawa da Turji, inda ya ce tsoho ne ba na yanzu ba ne.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.