Rai Bakon Duniya: Basarake kuma Kawun Mai Martaba Sarki Ya Rasu a Gombe

Rai Bakon Duniya: Basarake kuma Kawun Mai Martaba Sarki Ya Rasu a Gombe

  • Jihar Gombe ta yi babban rashi bayan sanar da rasuwar daya daga cikin sarakunanta wanda ya ba al'umma gudunmawa
  • Tsohon minista a Najeriya, Farfesa Isa Ali Pantami ya tura ta’aziyyarsa kan rasuwar Hakimin Wuro Tale, Alhaji Adamu Yerima
  • Majiyoyi sun tabbatar da cewa marigayin ya rasu ne a yankin karamar hukumar Dukku da ke jihar Gombe

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Dukku, Gombe - Tsohon ministan sadarwa a Najeriya, Farfesa Isa Ali Pantami ya tura sakon ta'aziyya bayan rashin basarake a Gombe.

An bayyana cewa marigayin ya rasu ne a yankin karamar hukumar Dukku da ke jihar Gombe inda aka yaba da gudunmawar da ya bayar.

Pantami ya jajanta bayan rasuwar basarake a Gombe
Farfesa Isa Ali Pantami da Sarkin Dukku. Hoto: Prof. Isa Ali Pantami.
Source: Facebook

Pantami ya jajanta bayan rasuwar Hakimi a Gombe

Farfesa Pantami ya mika sakon ta'aziyyar a shafinsa na Facebook a yau Alhamis 6 ga watan Nuwambar shekarar 2025 da ke ciki.

Kara karanta wannan

'An rasa jigo a Najeriya,' Tinubu kan rasuwar tsohon gwamna, Janar Mohammed

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Pantami ya yi ta’aziyya ta musamman kan rasuwar Hakimin Wuro Tale, Alhaji Adamu Yerima, wanda Allah ya rasu a Dukku.

Ya kuma tura sakon ga dangin marigayi da Mai Martaba Sarkin Dukku, Alhaji Haruna Abdulqadir Rashid II.

Sheikh Pantami ya ce marigayin shi ne kawun Mai Martaba Sarkin Dukku wanda kuma shi ne Hakimin Wuro Tela a masarautar da ke jihar Gombe.

Pantami ya yi addu'o'i ga marigayi Hakimin Wuro Tale
Farfesa Pantami, Sarkin Dukku da marigayi Hakimin Wuro Tale. Hoto: Prof. Isa Ali Pantami.
Source: Facebook

Addu'o'in da Pantami ya yi ga marigayin

Tsohon minisan ya roƙi Allah ya gafarta masa, ya karɓe shi cikin aljannar Firdausi tare da iyayen da masoya da suka riga mu gidan gaskiya.

A cikin sanarwar, Pantami ya ce:

"Muna mika ta’aziyya ta musamman bisa rasuwar Hakimin Wuro Tale, Alhaji Adamu Yerima.
"Muna jajantawa dangin marigayi da kuma Mai Martaba Sarkin Dukku, Alhaji Haruna Abdulqadir Rashid II, bisa rasuwar kawunsa wanda kuma shi ne Hakimin Wuro Tale.
"Allah ya ji kansa, ya sanya shi cikin Jannatul Firdausi, tare da iyayenmu da masoyanmu da suka rigamu gidan gaskiya."

Kara karanta wannan

Najeriya ta yi rashi, tsohon gwamna, NSA, Janar Mohammed ya rasu

Martanin masu ta'ammali da kafofin sadawa

Mutane da dama sun taya Pantami jimami bayan rashin basaraken da aka yi a jihar Gomne inda suka ta yi masa addu'o'i.

Daga cikin wadanda suka yi martani akwai masu yi masa godiya bisa ta'aziyyar da ya yi musu a matsayinsu na yan karamar hukumar Dukku ko kuma kusanci da suke da shi da marigayin.

Gurama A Gurama ya ce:

"Amin ya Allah! mun gode sosai ya Sheikh."

Aliyu Moh D Rasheed:

"Amin ya Allah, muna godiya ya Sheikh, muna matukar godiya."

Lukman Umar:

"Amin, amma ba kawunsa ba ne, dan uwansa ne."

Pantami ya yi jimamin rasuwar Sheikh Jingir

A baya, kun ji cewa tsohon minista a Najeriya, Farfesa Isa Ali Pantami ya shiga alhini bayan rasuwar malamin Izala, Sheikh Sa'idu Hassan Jingir, wanda aka sanar da rasuwarsa.

Pantami ya aika da ta’aziyya ga iyalan mamacin, almajiransa, ‘yan uwa da Sheikh Muhammad Sani Yahaya Jingir tare da shugabanni baki daya a Najeriya.

Kara karanta wannan

Daga shiga APC, Gwamna Diri ya yi wa Tinubu alkawarin kaso 99 na kuri'u a zaben 2027

Tsohon ministan ya ce marigayin ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen addini, don haka rasuwarsa babban rashi ne ga al’umma da daukacin Musulmi.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.