Tashin Hankali: An Kama Bindigogi da Mugayen Makamai Ana Shirin Shiga da Su Zamfara

Tashin Hankali: An Kama Bindigogi da Mugayen Makamai Ana Shirin Shiga da Su Zamfara

  • Dakarun rundunar kare al'umma da gwamnatin Zamfara ta dauka (CPG) sun samu nasara a kokarinsu na kare rayuka da dukiyoyin jama'a
  • Ankarawan Zamfara sun kama wata mota dauke da makamai ciki har da bindigogi kirar AK47 da ake zaton na yan bindiga ne
  • Direban motar da aka kama dauke da makaman ya ce bai san komai ba, yana mai cewa wata mata ce ta dora kayan daga tashar Gusau

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Zamfara - Jami'an tsaro na rundunar Community Protection Guard (CPG) wadanda gwamnatin Zamfara ta kirkiro domin yakar matsalar tsaro sun kama makamai.

Kara karanta wannan

Kama dalibin jami'ar da ya soki gwamna a Facebook ya fara tayar da kura a jihar Neja

Dakarun CPG da aka fi sani da Askarawan Zamfara sun cafke mugayen makamai da suka hada da bindigogi da alburusai, wadanda ake kyautata zaton za a shiga da su jihar domin kai wa yan bindiga.

Jihar Zamfara.
Hoton taswirar jihar Zamfara Hoto: Legit.ng
Source: Original

Rahoton Leadership ya nuna cewa dakarun tsaron sun kama makaman ne a cikin wata mota lokacin da suke aikin binciken ababen hawa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ankarawa sun kama makamai a Zamfara

Rahotanni daga yankin sun nuna cewa daga cikin makaman da jami'an tsaron suka gano a cikin motar akwai bindigogi biyu kirar AK-47, RPG ɗaya, da kuma wasu alburusai da dama.

Wani jami’in rundunar tsaro ta CPG da ya bayyana sunansa da Salisu Adamu, ya ce sun kama motar ne a lokacin da suke gudanar da binciken tsaro na yau da kullum a kauyen Dangulbi.

“An ɓoye makaman ne a cikin kwalaye da aka cika da kifi ta yadda ba za a yi zargin da wani abu daban a ciki ba.
"Lokacin da muka nemi mu bincika motar, direban ya fara nuna ba sai an yi hakan ba amma muka dage, sai muka gano abin da ke cikin wadannan kwalaye” in ji Adamu.

Kara karanta wannan

Sojoji sun gwabza da 'yan bindiga a Kano, an samu asarar rayuka

Yadda direban mota ya dauko makamai

Direban motar da jami'an CPG suka kama, Bashar Mustapha, ya tabbatar da cewa an samu wadannan mugayen makamao ne a motarsa, amma ya yi ikirarin cewa ba nasa bane.

A cewarsa, ya ɗauko fasinjoji da kaya ne daga wata tasha ta Gusau zuwa Magami, kafin jami’an CPG su tare shi a daidai kauyen Dangulbi, cewar rahoton Daily Post.

“Makaman na cikin wawu kaya ne da wata mata ta ɗora daga Gusau. Ni ban san abin da take ɗauke da shi ba,” in ji Mustapha.
Gwamnan Zamfara.
Hoton Gwamna Dauda Lawal a wurin kaddamar da Askarawan Zamfara Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Rahotanni sun ce an mika motar tare da makaman da aka kama ga hukumomin tsaro domin ci gaba da bincike.

Gwamnan Zamfara ya yi gargardi kan sulhu

A wani labarin, kun ji cewa gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi gargadi kan hawa teburin sulhu da ake yi da 'yan bindiga ba tare da sun ajiye makamai ba.

Gwamna Dauda ya yi gargadin cewa sulhun da ke barin kungiyoyin ‘yan bindiga da makaman su tare da ba su damar sa sharudda, ba zai magance tashin hankalin da ake ciki ba.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta ware kusan N5bn don wasu muhimman ayyuka

Ya ce abubuwan da ke faruwa a Zamfara, suna nuna irin kalubalen da ake fuskanta a sassa da dama na Najeriya​ da ma nahiyar Afirka baki ɗaya wajen neman zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262