'Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokoki a Kebbi
- 'Yan bindiga dauke da makamai sun yi ta'asa a jihar Kebbi bayan sun kai wani harin da ya ritsa da babban jami'in gwamnati
- Tsagerun 'yan bindigan sun yi awon gaba da mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kebbi da suka kai hari a garinsa
- 'Yan bindigan sun sace mataimakin shugaban majalisar ne lokacin da yake kan hanyarsa ta komawa gida da ya kammala sallah a masallaci
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Kebbi - Wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun sace mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kebbi, Hon. Samaila Bagudu.
Miyagun 'yan bindigan sun sace mataimakin shugaban majalisar ne a garinsa na Bagudu da ke cikin karamar hukumar Bagudu ta jihar Kebbi.

Source: Facebook
Rahoton tashar Channels tv ya bayyana cewa maharan sun kai farmakin ne a garin Bagudu da yammacin Jumma’a, 31 ga watan Oktoban 2025.
'Yan bindiga sun kai hari a Kebbi
'Yan bindigan sun rika harbe-harbe babu kakkautawa domin tsoratar da jama’a a yayin harin da suka kai.
A cewar majiya daga yankin, an sace mataimakin shugaban majalisar dokokin ne jim kadan bayan ya kammala sallah, kuma yana kan hanyarsa ta komawa gida daga masallaci.
Me hukumomi suka ce kan lamarin?
Mai magana da yawun gwamnatin jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa gwamnati tana bin diddigin al’amarin, rahoton jaridar The Punch ya tabbatar da labarin.
Sai dai, bai yi wani cikakken bayani ba kan yadda lamarin ya auku.
Hakazalika, ba a samu jin ta bakin rundunar 'yan sandan jihar Kebbi ba kan aukuwar lamarin.
Kokarin samun karin bayani daga rundunar ‘yan sandan jihar ya ci tura har zuwa lokacin kammala hada wannan rahoton.

Source: Original
Rahotanni sun nuna cewa mazauna garin sun shiga firgici bayan harin, yayin da jami’an tsaro ke cigaba da neman hanyoyin kubutar da mataimakin kakakin tare da tsaurara tsaro a yankin.

Kara karanta wannan
'Tinubu zai rika karbar harajin shakar iska a Najeriya,' 'Dan takarar Shugaban Kasa a SDP
Harin dai ya nuna yadda 'yan biindiga ke ci gaba da cin karensu babu babbaka duk da kokarin da gwamnati da hukumomin tsaro ke yi wajen samar da tsaro.
Jihar Kebbi na daya daga cikin jihohin yankin Arewa maso Yamma masu fama da matsalar raahin tsaro wadda 'yan bindiga da 'yan ta'adda suka haifar.
Karanta wasu labaran kan 'yan bindiga
- 'Yan bindiga sun kashe basarake da wasu mutane bayan kai hari a Sokoto
- Yan bindiga sun farmaki masu sallah, sun yanke kan wani da ke kokarin tserewa
- Yan bindiga sun sace masu ibada 20, sun hallaka malamin addini a Kaduna
- 'Yan sanda sun cafke 'yan bindiga a Kano bayan fara kai hare hare
Sojoji sun hallaka 'yan bindiga a Kebbi
A wani labarin kuma, kun ji cewa dakarun sojoji sun samu gagarumar nasara yayin wani artabu da suka yi da 'yan bindiga a jihar Kebbi.
Dakarun sojojin sun samu nasarar hallaka 'yan bindiga fiye da 80 bayan sun yi yunkurin shigowa jihar Kebbi daga Zamfara.
Hakazalika, sojojin sun yi nasarar kwato babura da dama tare da ceto wasu daga cikin mutanen da 'yan bindigan suka sace.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
