Tinubu Ya ba Hafsoshin Tsaro Aiki, Ya Bukaci Su Murkushe Barazanar da Ta Taso a Najeriya

Tinubu Ya ba Hafsoshin Tsaro Aiki, Ya Bukaci Su Murkushe Barazanar da Ta Taso a Najeriya

  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karrama hafsoshin tsaro da matsayi a wani taro da aka shirya a fadar shugaban kasa da ke Abuja
  • Tinubu ya ce bullar kungiyoyin yan bindiga a Arewa ta Tsakiya da Arewa ta Yamma ne baranazar da ta damu gwamnatinsa
  • Ya bukaci hafsoshin tsaron su tashi tsaye su tunkari duk wata barazana, domin yan Najeriya na son ganin zaman lafiya ya dawo

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bukaci hafsoshin tsaro da su tashi tsaye wajen magance barazanar tsaro da ke kara tasowa a sassa daban-daban na Najeriya.

Kara karanta wannan

Atiku ya yi martani bayan Tinubu ya sassauta hukuncin Maryam Sanda

Shugaba Tinubu ya fadi haka ne a yayin da yake karrama sababbin hafsoshin tsaro da matsayi fadar shugaban kasa da ke Abuja, yau Alhamis.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Hoton Shugaba Bola Ahmed na jagorantar taro a fadar shugaban kasa Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X.

Abin da Tinubu ya fadawa hafsoshin tsaro

Da yake jawabi a taron, Tinubu ya ce barazanar tsaro na ci gaba da sauyawa da kuma bayyana a wasu siffofi, musamman a yankunan Arewa ta Tsakiya, Arewa maso Yamma da kuma wasu sassan Kudancin Najeirya.

“Barazanar tsaro na kara sauyawa, tana ƙaruwa, kuma abin da ke damun wannan gwamnati shi ne bullar sababbin ƙungiyoyin ’yan bindiga a yankunan da ke fama da tashin hankali.
"Ba za mu bari wadannan barazana su samu kafa ba. Dole mu yi gaggawa, mu murkushe su tun kafin su girma,” in ji Shugaban Ƙasa.

Tinubu ya ƙara da cewa ’yan Najeriya sun kosa su ga zaman lafiya da tsaro sun dawo, don haka ya bukaci hafsoshin tsaron su yi aikinsu da cikakken kishin ƙasa da sadaukarwa.

Kara karanta wannan

Aiki ga mai kare ka: Badaru ya gana da hafsoshin tsaro, ya ja kunnensu

"Ina umartar ku a matsayinku na shugabannin rundunonin tsaron Najeriya da ku yi aiki da ƙwazo da jajircewa.
"Yan ƙasa suna buƙatar ganin sakamako, ba uzuri ba. Mun kagara mu fara murnar dawowar zaman lafiya."

- Bola Tinubu.

Tinubu ya daga darajar hafsoshin tsaro

Taron kara wa manyan shugabannin sojojin matsayi ya gudana ne a dakin taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya da ke fadar shugaban kasa.

A makon da ya gabata, Shugaba Tinubu ya gudanar da sauye-sauye a tsarin tsaron ƙasar, inda ya nada sababbin hafsoshin tsaro, cewar rahoton Daily Trust.

A taron yau Alhamis, Olufemi Olatubosun Oluyede ya tashi daga matsayin Laftanar Janar ya koma Janar bayan nada shi a matsayin babban hafsan tsaro na kasa (CDS).

Shugaba Tinubu da Hafsoshin Tsaro.
Hoton Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da hafsoshin tsaro a Aso Rock Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Shugaban hukumar leken asiri (DIA), Emmanuel Undiendeye Undiendeye ya tashi daga matsayin Manjo Janar, ya zama Laftanar Janar a rundunar sojoji.

Sauran su ne Hafsan Rundunar Sojijin Kasa, wanda ya tashi daga Manjo Janar ya zama Laftanar Janar Waidi Shaibu da Hafsan Sojojin Sama wanda ya tashi daga Air Vice Marshal, zuwa Air Marshal Kevin Aneke.

Kara karanta wannan

Bayan karbar bukatar Tinubu, majalisa ta sa lokacin tantance sababbin hafsoshin tsaro

Na karshe shi ne Rear Admiral, wanda yanzu ya zama Admiral Idi Abbas bayan nada shi a matsayin Hafsan Rundunar Sojojin Ruwa.

Hafsan sojojin sama ya yi alkwari

A wani rahoton, kun ji cewa shugaban rundunar sojin sama ta Najeriya (NAF), Sunday Kelvin Aneke, ya yi alkawarin jagorantar runduna mai fasaha, ladabi, da kwarewa.

Air Vice Marshall din ya bayyana cewa zai jagoran rundunar da za ta hana ‘yan ta’adda sakat ballantana su samu damar shirya kai hare-hare kan jama'a

Aneke ya jaddada cewa manufarsa ita ce gina rundunar da za ta rika amsa kiran gaggawa a kan lokaci tare da kai hari daidai da ka’ida.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262