‘Su Suka Zagaye Shi’: Gwamna Ya Tona Yadda ’Yan Siyasa Suka Munafurci Buhari

‘Su Suka Zagaye Shi’: Gwamna Ya Tona Yadda ’Yan Siyasa Suka Munafurci Buhari

  • Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya ce tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kewaye kansa da masu kwaɗayi
  • Sule ya bayyana yadda wasu ’yan siyasa ke yaba wa shugabanni yayin da suke mulki, amma suna juya baya da zarar sun bar ofis
  • Ya kuma yaba wa marigayi Raymond Dokpesi saboda jarumtar sa wajen kafa gidan rediyo da talabijin na farko mai zaman kansa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya bayyana yadda marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya hadu da munafukai.

Abdullahi Sule ya ce Muhammadu Buhari ya kewaye kansa da masu kwaɗayi lokacin da yake mulki wanda suke zuga shi ba don Allah ba.

Gwamna ya fadi yadda munafukai suka mamaye Buhari
Gwamna Sule da marigayi Muhammadu Buhari. Hoto: Abdullahi Sule Mandate, Muhammadu Buhari.
Source: Facebook

Rahoton Punch ya ce Gwamnan ya bayyana hakan ne a taron tattaunawa da cibiyar “Raymond Dokpesi” ta shirya a Abuja.

Kara karanta wannan

ADC ta aika sako mai zafi ga Tinubu kan sauya hafsoshin tsaro

'Yadda yan siyasa suka munafurci Buhari'

Sule ya ce ya shaida da idonsa yadda ’yan siyasa ke yaba wa Buhari a ofis, amma suka watsar da shi bayan ya sauka daga mulki.

Ya ce:

“A matsayin Gwamna, na ga yadda kwaɗayi ke lalata zama na gaskiya. Ana cewa Buhari ya fi kowa, amma yanzu ana sukarsa.”

Gwamnan ya kara da cewa, bayan Buhari ya bar mulki, wadannan mutane da suka yaba masa su ne ke cewa shi ne mafi raunin shugaba a tarihi.

Gwamna ya yaba marigayi Dokpesi kan jijircewarsa

Sule, wanda aka karrama da lambar yabo ta NIPR, ya ce yana girmama marigayi Dokpesi saboda jarumtar sa wajen kafa gidan talabijin a lokacin soja.

Ya ce, Dokpesi ya kafa tashar rediyo da talabijin mai zaman kanta a wani lokaci da gwamnati ke da iko a kan yawancin kafafen watsa labarai.

“Ina taya murna da marigayi Dokpesi wanda bai taɓa tsoron faɗa wa gwamnati gaskiya ba, ko da a lokutan wahala.”

Kara karanta wannan

Nnamdi Kanu: Wike ya fadi sharadin zama shaidan shugaban IPOB a kotu

- Gwamna Abdullahi Sule

Gwamna ya yi magana kan yadda Buhari ya sha fama da munafukai
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule. Hoto: Abdullahi A.Sule Mandate.
Source: Facebook

An yabawa Gwamna Sule kan kyautar fili

Shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, ya gode wa Gwamna Sule saboda ba hukumar fili domin gina jami’ar hulɗa da jama’a ta duniya a jihar Nasarawa.

Neliaku ya bayyana cewa aikin ginin jami’ar ya kai matakin cigaba sosai, inda za ta zama cibiyar horas da shugabanni masu hangen nesa.

A cewarsa, jami’ar za ta zama cibiyar koyar da dabarun sadarwa mai inganci da haɗa manufofi da aikace-aikace a Najeriya, cewar Daily Post.

Taron, wanda aka shirya domin girmama marigayi Dokpesi, ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, masana harkokin yada labarai da kwararrun masu hulɗa da jama’a.

Gwamna ya fadi dalilin gwamnoni na shiga APC

Kun ji cewa Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya yi tsokaci kan sauya shekar da wasu gwamnoni da wasu 'yan siyasa ke yi zuwa jam'iyyar APC.

Abdullahi Sule ya bayyana cewa sauya shekar da ake gani daga wajen gwamnonin da fitattun 'yan siyasa, na faruwa ne saboda manufofin Bola Tinubu.

Kara karanta wannan

EFCC ta fadi abin da za ta yi kan tuhumar tsohon gwamna da ya koma APC

Gwamnan ya bayyana cewa manufofin da gwamnatin shugaban kasan ke aiwatarwa na bukatar matukar jarumta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.