Ta Faru Ta Kare: Majalisa Ta Amince da Kirkirar Karin Jiha 1 a Najeriya

Ta Faru Ta Kare: Majalisa Ta Amince da Kirkirar Karin Jiha 1 a Najeriya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Kwamitin hadin gwiwa na majalisar dattawa da wakilai kan gyaran kundin tsarin mulki ya amince da kafa sabuwar jiha.

Kwamitin ya amince da hakan ne kan kirkirar sabuwar jihar a yankin Kudu maso Gabas domin tabbatar da adalci da daidaito.

Majalisun tarayya sun amince da kirkirar sabuwar jiha a Najeriya
Shugaban majalisar dattawa, Gidswill Akpabio da kakakin majalisa, Tajudeen Abbas. Hoto: The Nigerian Senate.
Source: Twitter

Za a karawa yanki 1 jiha a Najeriya

An cimma matsayar ne a taron kwanaki biyu da aka gudanar a Legas, inda aka duba bukatu 55 na neman sababbin jihohi, cewar Vanguard.

Kara karanta wannan

Sanata Ned Nwoko ya fadi abubuwa 2 da za su dawo da zaman lafiya Kudu maso Gabas

Wannan mataki zai karawa yankin jiha daya, wanda zai zama jihohi shida gaba daya, domin daidaitawa da sauran yankuna na kasar.

A halin yanzu, yankin Kudu maso Gabas yana da jihohi biyar kacal, wanda ya gaza adadin da ke cikin sauran yankuna na Najeriya.

Barau ya jagoranci kwamitin kafa sabuwar jiha a Najeirya
Mataimakin shugaban majalsar dattawa, Sanata Barau Jibrin. Hoto: Barau I Jibrin.
Source: Facebook

Waye ya jagoranci kwamitin kirkirar sabuwar jiha?

Taron da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya jagoranta, ya tattauna sosai kan bukatar kafa karin jiha.

Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, wanda ya jima yana fafutukar batun, ya ce bukatar tana da tushe a adalci da daidaito.

‘Yan kwamitin sun amince da bukatar kafa sabuwar jiha a yankin bayan tattaunawa mai zurfi da shawarwari tsakanin membobin majalisar.

Sanata Abdul Ningi daga Bauchi ta Tsakiya ne ya gabatar da kudirin, yayin da Ibrahim Isiaka daga Ogun ya mara masa baya a majalisar.

Goyon baya da kudirin ke samu a majalisa

Kudirin ya samu cikakken goyon bayan mambobin kwamitin, wanda hakan ya tabbatar da amincewa da kafa sabuwar jiha a yankin.

Kara karanta wannan

Abu ya girma: Majalisa ta amince da kirkirar jihohi 6 a Najeriya

Bayan haka, kwamitin ya kafa wani karamin kwamitin domin duba bukatun kafa sababbin jihohi da kananan hukumomi a fadin kasa.

An bayyana cewa kwamitin ya karɓi sama da bukatu 278 daga sassa daban-daban na kasar domin duba yiwuwar kafa sababbin yankuna.

Sanata Barau Jibrin ya bukaci ‘yan majalisa da na jihohi su hada kai don tabbatar da nasarar wannan kuduri yayin kada kuri’u, Punch ta tabbatar da rahoton.

Ya ce dole ne a samu hadin kan dukkan bangarori na gwamnati domin cimma burin kafa karin jihohi cikin tsarin adalci da gaskiya.

“Dole mu ƙarfafa abin da muka fara domin dukkan sassan ƙasar su shiga cikin wannan tsari.”

- Sanata Barau Jibrin

Majalisa ta fara bitar kirkirar jihohi 55

Mun ba ku labarin cewa Majalisar dattawa ta tabbatar da aniyar yin gyare-gyaren da za su amfanar da al’umma a kundin tsarin mulki na 1999.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya bayyana matakan da ake dauka a halin yanzu.

A taron bitar kwana biyu da aka gudanar a Legas, an tattauna kan bukatun kirkirar jihohi, gundumomi da sauransu domin inganta shugabanci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.