EFCC Ta Kwato N500bn a Mulkin Tinubu, Shettima Ya Fadi inda Aka Kai Kudin

EFCC Ta Kwato N500bn a Mulkin Tinubu, Shettima Ya Fadi inda Aka Kai Kudin

  • Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ta samu nasarori masu tarin yawa a yakin da take yi a Najeriya
  • Kashim Shettima ya bayyana cewa hukumar ta samu nasarar kwato biliyoyin kudi cikn shekara biyu na mulkin Shugaba Bola Tinubu
  • Mataimakin shugaban kasan ya nuna cewa hukumar ta kuma samu nasarar gurfanar da dubunnan mutane a gaban kotu

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana nasararorin da hukumar yaki da cin hanci ta EFCC ta samu a karkashin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Kashim Shettima ya bayyana cewa EFCC ta samu nasarar tara dukiyar da ta kai Naira biliyan 500 cikin shekaru biyu da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi a kan mulki.

Shettima ya fadi nasarorin da EFCC ta samu
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima. Hoto: @stanleynkwocha
Source: Twitter

Tashar Channels tv ta ce Kashim Shettima ya bayyana hakan ne yayin bude taron bita da horas da alkalai karo na bakwai wanda EFCC da cibiyar NJI suka shirya a Abuja.

Kara karanta wannan

Kudirori 6 da Tinubu ya yi fatali da su, ya ki rattabawa hannu su zama doka'

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mataimakin shugaban kasan ya wakilci Mai girma Bola Tinubu a wajen taron, rahoton jaridar The Punch ya tabbatar da hakan.

Tinubu bai yi wa EFCC katsalandan

Kashim Shettima ya ce manufar gwamnatin Tinubu ta rashin tsoma baki a harkokin hukumomin yaki da rashawa ta taimaka wajen karfafa yaki da cin hanci da kuma inganta gaskiya a hukumomin gwamnati.

“A matsayin gwamnati, mun fifita gaskiya da rikon amana ta hanyar karfafa hukumomin yaki da rashawa da kuma ba su cikakken ’yanci wajen aiwatar da aikinsu yadda doka ta tanada."

- Kashim Shettima

Ya ce wannan yanayi na aiki cikin ’yanci ya bada damar samun ci gaba mai yawa cikin shekaru biyu da suka gabata.

“Misali, EFCC ta samu nasarar gurfanar da sama da mutum 7,000 a gaban kotu kan laifin rashawa kuma ta kwato kadarori da kudi fiye da Naira biliyan 500.”

- Kashim Shettima

Ina ake kai kudin da aka kwato?

Kara karanta wannan

Wike na shirin yin takara da Tinubu a 2027? An ji gaskiyar zance

Shettima ya kara da cewa kudin da aka kwato daga hannun barayin gwamnati ana mayar da su cikin tattalin arzikin kasa domin tallafa wa shirye-shiryen cigaba kamar bada lamuni ga dalibai da shirin bayar da rance ga ’yan kasa.

“Kudin da EFCC ta kwato daga aikata laifuffuka ana amfani da su wajen tallafawa muhimman shirye-shiryen jin kai, ciki har da bada lamuni ga dalibai da tsarin bashi ga masu karamin karfi."

- Kashim Shettima

EFCC ta kwato kudade daga hannun barayi
Shugaban EFCC na kasa, Ola Olukoyede Hoto: @OfficialEFCC
Source: Facebook

Shugaba Tinubu bai kare 'yan siyasa

Ya kuma jaddada cewa gwamnatin Tinubu ba ta kare kowa daga bincike ko gurfanarwa.

“Babu wani mutum ko kungiya da za ta iya cewa wannan gwamnati na kare ’yan siyasa. Mun ba kotuna da hukumomin yaki da rashawa cikakken iko don su aiwatar da aikinsu cikin gaskiya da adalci."

- Kashim Shettima

EFCC ta gayyaci shugaban NAHCON

A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar EFCC ta gayyaci shugaban hukumar kula da Alhazai ta kasa (NAHCON), Farfesa Saleh Abdullahi Usman.

Hukumar EFCC ta gayyaci shugaban na NAHCON ne bisa zargin karkatar da kudi da suka kai sama da Naira biliyan 50 da suka shafi shirye-shiryen aikin Hajjin 2025.

Kara karanta wannan

Bayan shan suka, gwamnatin Tinubu ta yi magana kan sakin Maryam Sanda da sauran masu laifi

Daga cikin kudin da ake zargi an karkatar akwai Naira biliyan 25 da aka kashe wajen biyan haya da gina tantuna a kasar Saudiyya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng