Wata Sabuwa: An Dakatar da Shugaban Jam'iyyar APC Mai Mulki

Wata Sabuwa: An Dakatar da Shugaban Jam'iyyar APC Mai Mulki

  • Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta dauki matakin ladabtarwa kan daya daga cikin mutanen da ke jan ragamar shugabancinta a jihar Edo
  • An dakatar da shugaban jam'iyyar APC a wata mazaba da ke karamar hukumar Etsako ta Gabas a jihar Edo
  • Jam'iyyar APC ta bayanin dalilin dakatar da shugaban wanda ta bada umarnin a hana shi halartar duk wasu tarurruka da suka dangance ta

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Edo - Jam’iyyar APC mai mulki ta dakatar da daya daga cikin shugabanninta a jihar Edo.

Jam'iyyar APC ta dakatar da Mallam Adamu Ototobor, wanda shi ne shugaban mazaba ta 9 a karamar hukumar Etsako ta Gabas a jihar Edo, daga duk wata harkar jam’iyyar har sai an samu wani sabon umarni.

Jam'iyyar APC ta dakatar da shugabanta
Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda Hoto: @OfficialAPCNg
Source: Twitter

Jaridar The Nation ta ce dakatarwar ta fito ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar APC na jihar Edo, Prince Peter Uwadiae, wadda ya fitar a ranar Asabar, 18 ga watan Oktoban 2025.

Kara karanta wannan

MCAN: 'Yan NYSC Musulmi sun yi taron Arewa maso Gabas a Gombe

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa APC ta dakatar da shugabanta a Edo?

Sanarwar ta bayyana cewa dakatarwar da aka yi wa shugaban na APC za ta fara aiki ne nan take.

A cewar sanarwar, an dakatar da Ototobor ne bayan binciken halayensa da ayyukansa na baya-bayan nan, wadanda jam’iyyar ta ce ba su daidaita da tsarin ladabi, biyayya da dokokin jam’iyyar a jihar Edo.

“An umurci shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Etsako ta Gabas da ya hana Mallam Adamu Ototobor halartar ko shiga cikin kowane taro, zama ko wani taron jam’iyya har sai lokacin da aka dage dakatarwarsa a hukumance.”

- Prince Peter Uwadiae

Jam’iyyar ta kuma jaddada cewa ladabi, biyayya da girmama hukumomi sune ginshikin APC, kuma duk wani aiki da zai iya lalata waɗannan kimomi ba za a lamunta da shi ba.

An dakatar da shugaban APC a Edo
Taswirar jihar Edo, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Karanta wasu karin labaran kan jam'iyyar APC

Kara karanta wannan

ADC ta yi babban kamu, tsohon shugaban PDP ya yi murabus bayan shekaru 22

Uba Sani ya ce APC za ta samu kuri'u

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya yi magana kan babban zaben shekarar 2027 da ake tunkara.

Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa jam'iyyat APC za ta samu kuri'u kaso 95% cikin 100% a jihar Kaduna a zaben shekarar 2027.

Ya bada tabbacin cewa babu sauran wata adawa a jihar Kaduna domin duk mafi yawancinsu sun sauya sheka zuwa jam'iyya mai mulki.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng