Auren Gata: Ma'aurata a Kano Sun Roƙi Gwamna Abba Alfarma domin Samun Dama

Auren Gata: Ma'aurata a Kano Sun Roƙi Gwamna Abba Alfarma domin Samun Dama

  • Wasu maza magidanta a Kano sun nuna sha'awarsu kan shirin auren gata da gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta shirya domin rage gwauraye
  • Ma'auratan sun roƙi Gwamna Abba Kabir Yusuf ya haɗa su cikin shirin bikin auren da gwamnatin Kano ta shirya domin su iya ƙara mata
  • Hukumar Hisbah ta tabbatar da cewa gwamnati na shirin auren ga kimanin mutane 2,000, kuma za a yi gwajin lafiya don inganta tarbiyya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Gwamnatin jihar Kano ta bayyana shirin gudanar da bikin auren gata ga mata da maza 2,000, wanda ya jawo hankalin wasu mazan aure.

Wasu mazan aure a jihar sun roƙi Gwamna Abba Kabir Yusuf da ya ba su damar shiga shirin domin su ƙara aure kamar yadda addini ya halatta.

Kara karanta wannan

Kano: 'Dan jarida ya debo ruwan dafa kansa, ICPC ta kama shi kan zambar N14m

Ma'aurata a Kano sun roki Abba Kabir ya saka su cikin tsarin auren gata
Gwamna Abba Kabir da wadanda aka yi wa auren gata a Kano. Hoto: @abdullahayofel, @khaleeffah.
Source: Twitter

An tsara shirin da gwamnati ta dauki nauyi ne domin inganta tarbiyya, rage tsadar aure, da taimakawa matasa da zawarawa su samu aure cikin sauƙi, cewar rahoton Legit.ng.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hisbah ta fara shirin auren gata a Kano

Malam Mujahid Aminudeen, mataimakin kwamandan hukumar Hisbah, ya tabbatar da cewa ana shirye-shiryen gudanar da bikin tare da yin rajista da gwajin lafiya ga ma’aurata.

Ya ce wannan mataki zai taimaka wajen rage aikata laifuffuka kamar karuwanci da shan miyagun ƙwayoyi tare da ƙarfafa zaman lafiya a cikin iyalai.

Mazan auren sun fara neman shiga shirin

Sai dai yanzu maza da ke da mata ɗaya sun ce wannan dama ce gare su don su ƙara aure ba tare da wahalar kuɗin lefe da kayan ɗaki ba.

Wani ɗan kasuwa mai suna Ahmed Sani ya ce ya shafe shekaru ashirin da aure kuma yana son ƙara aure amma tsadar bukukuwa na hana shi.

Kara karanta wannan

Rigiji gabji: Atiku ya nemi a binciki Tinubu da ministocinsa kan takardun bogi

“Aure na biyu yana da lada, amma kuɗin lefe, kayan ɗaki, da kuɗin ɗaki suna da yawa, inda yake roƙon gwamnati ta taimaka."
Gwamna Abba Kabir zai sake kashe makudan kudi saboda auen gara
Gwamna Abba Kabir yayin wani taro a gidan gwamnatin Kano. Hoto: Abba Kabir Yusuf.
Source: Facebook

Martanin wasu mazauna Kano

Haka ma wani ma’aikaci, Musa Bello, ya ce shigar da maza aure cikin shirin zai taimaka wajen hana aikata badala a boye da kuma kare mutuncin mata.

Ya bayyana cewa:

“Idan mutum na da iko amma tsadar aure ta hana shi, hakan na iya jefa shi cikin zina, wanda ya fi muni.”

Wani direban mota, Ibrahim Garba, ya ce matarsa ma ta karfafa masa gwiwa ya ƙara aure domin samun taimako a kula da gida da ‘ya’ya.

Ya ce sun shirya yin gwajin lafiya tare da matar da yake so, yana roƙon gwamnati ta haɗa su a cikin wannan shirin mai albarka.

Gwamna Abba Kabir ya shirya sake auren gata

Mun ba ku labarin cewa gwamnatin Kano ta fara shirin daurar da marayu da marasa aure a cikin tsarinta na auren gata da aka saba gudanarwa lokaci zuwa lokaci a jihar.

A wannan karo na biyu da gwamnatin Abba Kabir Yusuf ke daukar nauyin auren, ta amince da Naira biliyan 1.6 domin tabbatar da komai ya tafi da kyau.

Kara karanta wannan

Kano ta dauki sabon kambu, ta zama ta 2 a tara kudin shiga a jihohin Najeriya

Daga cikin kudin, za a biya kudin lefe, kayan dakunan amarya da shirya bikin aure karkashin kulawar Ma'aikatar Harkokin Addini ta jihar.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.