Sojoji Sun Samu Gagarumar Nasara kan 'Yan Bindiga a Sokoto
- 'Yan bindiga dauke da muggan makamai sun kai wani harin ta'addanci a karamar hukumar Wurno da ke jihar Sokoto
- Miyagun sun kai harin ne da daddare inda suka bude wuta kan mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba
- Dakarun sojoji sun kai agajin gaggawa inda suka hallaka 'yan bindiga masu yawa tare da raunata wasu a kazamin artabun da suka yi
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Sokoto - Dakarun sojojin Najeriya na Operation Fansan Yanma sun hallaka ‘yan bindiga da dama a jihar Sokoto.
Dakarun sojojin sun hallaka 'yan bindigan ne yayin wani kazamin artabu da ya gudana a kauyen Sabon Garin Kwargaba, cikin karamar hukumar Wurno ta jihar Sokoto.

Source: Twitter
Masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama ne ya bayyana hakan a shafinsa na X.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
'Yan bindiga sun kai hari
Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a daren ranar Talata, 7 ga watan Oktoban 2025, da misalin karfe 11:30 na dare.
'Yan bindigan masu yawa dauke da muggan makamai sun kai farmaki a kauyen, inda suka rika harbi kan mai uwa da wabi domin tsoratar da mazauna yankin.
Sojoji sun ragargaji 'yan bindiga
Dakarun sojoji na rundunar Operation Fansan Yanma sun yi saurin zuwa wurin bayan sa suka samu kiran gaggawa.
Sojojin sun yi arangama da ‘yan bindigan a wani artabu mai tsanani wanda ya ɗauki mintuna da dama.
“An kashe ‘yan bindiga da dama yayin arangamar, yayin da wasu suka gudu dauke da raunukan harbin bindiga."
"Abin takaici, soja ɗaya da wata mace daga cikin mutanen kauyen sun rasa rayukansu a harin.”
- Wata majiya
Majiyar ta ƙara da cewa, an garzaya da wani soja da ya ji rauni a yayin harin zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Usmanu Danfodiyo (UDUTH), Sokoto, inda ake duba lafiyarsa.
An kuma tabbatar da cewa an tura karin jami’an tsaro zuwa yankin domin hana karin hare-hare da kuma dawo da zaman lafiya.
"Sojoji sun fara aikin zakulo ‘yan bindigar da suka tsere cikin daji, domin tabbatar da cikakken tsaro a yankin."
- Wata majiya

Source: Original
Abin a yaba ne
Wani mazaunin Sokoto, Usman Abubakar, ya yaba kan nasarar da dakarun sojojin suka samu kan 'yan bindiga.
"Wannan abin a yaba ne. Muna fatan za su ci gaba da kara kaimi don murkushe miyagu."
"Suna bakin kokarinsu, muna rokon Allah ya ci gaba da ba su nasara a aikin da suke yi."
- Usman Abubakar
Karanta wasu labaran kan dakarun sojoji
- Ana batun sulhu, dakarun sojoji sun dakile harin 'yan bindiga a Katsina
- Sojoji sun gwabza kazamin fada da 'yan bindiga, an samu asarar rayuka
- Abin da ka shuka: An yanke wa wasu manyan Sojojin Najeriya 3 hukuncin daurin rai da rai
- 'Yan ta'adda sun tilastawa sojoji tserewa bayan kai hari a Borno
Sojoji sun fafata da 'yan ta'adda
A wani labarin kuma, kun ji cewa dakarun sojoji sun yi artabu da 'yan ta'adda a jihar Taraba da ke yankin Arewa maso Gabas na Najeriya.
Sojojin na rundunar 6 Brigade na Operation Whirl Stroke, sun yi nasarar dakile harin da ‘yan ta’adda suka kai a kauyen Tor-Ikyeghgba, jihar Taraba.
Kwamandan rundunar, Brig. Janar Kingsley Uwa, ya yaba wa jaruntakar dakarun bisa kwazon da suka nuna da kuma saurin kai daukin da suka yi.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Asali: Legit.ng


