Muhimman Abubuwa kan Sabuwar Shugabar Rikon INEC da Aka Haifa a Kano
- May Agbamuche-Mbu ta karɓi ragamar shugabancin hukumar INEC bayan tafiyar Farfesa Mahmood Yakubu a makon nan
- Rahotanni sun bayyana cewa sabuwar shugabar rikon ta fito ne daga jihar Delta amma an haife ta a yankin Arewa, jihar Kano
- Agbamuche-Mbu lauya ce mai gogewar shekaru fiye da 30 da ke da ƙwarewa a harkokin doka da gudanarwa a Najeriya
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
FCT, Abuja – Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta sanar da cewa May Agbamuche-Mbu ta karɓi ragamar aiki a matsayin mukaddashiyar shugabar hukumar.
Hakan na zuwa ne bayan bayan ajiye aikin Farfesa Mahmood Yakubu da ke daf da kammala wa'adin shekara 10 a hukumar.

Source: Facebook
Daily Trust ta hada wani rahoto game da May Agbamuche-Mbu jim kadan bayan karbar ragamar hukumar INEC.

Kara karanta wannan
INEC: Yakubu ya fadi dalilin ajiye aiki, Tinubu ya shirya nada magajinsa makon nan
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
An gudanar da miƙa mata mulki ne a lokacin taron da aka yi da kwamishinonin zaɓe na jihohi (RECs) a hedkwatar hukumar da ke Abuja a ranar Talata.
An haifi May Agbamuche-Mbu a Kano
An haifi Agbamuche-Mbu a Kano amma asalinta 'yar asalin jihar Delta ce, sai dai ta yi wani bangare na rayuwarta a Arewa.
Ta halarci makarantar St. Louis da ke Kano kafin ta tafi jami’ar Ife (wanda yanzu ake kira jami'ar Obafemi Awolowo), a nan ta yi digiri a shekarar 1984.
Ta fara aiki a kotun kolin Najeriya a 1985 sannan daga baya ta zama lauya a Kotun Koli ta Ingila da Wales bayan ta kammala karatu a College of Law, London.
Kwarewa da aikin gwamnati da ta yi
Kafin ta shiga INEC, Agbamuche-Mbu ta kasance babbar lauya kuma abokiyar kafa kamfanin Norfolk, wani sanannen ofishin lauya da ke Legas.
Rahoton TVC ya nuna cewa ta yi aiki a matsayin lauya guda daya tilo a kwamitin tantance ayyukan fadar shugaban ƙasa tsakanin 2010 zuwa 2011.
Bayan haka, ta shiga kwamitin ministoci da ya tsara taswirar ci gaban sashen ma’adinai a 2016, kafin daga baya ta zama kwamishiniyar ƙasa a hukumar INEC a shekarar 2016.
Gudunmawa a fannin doka da zaɓe
A matsayin ta na kwamishina, ta taka muhimmiyar rawa wajen sauye-sauyen tsarin doka, haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki, da kuma ƙirƙirar manufofin gudanar da zaɓe a Najeriya.
Ta kuma kasance ƙwararriya a harkar sasanta rikice-rikice, inda ta rike mukamin sakatariya a Cibiyar Lauyoyi Masu Sasanta Rikici ta Najeriya.

Source: Twitter
A wajen rubuce-rubuce kuwa, ta wallafa fiye da makaloli 120 a jaridar This Day tsakanin 2014 zuwa 2016, inda ta tattauna batutuwan doka, mulki da tsare-tsaren gwamnati.
Shugaban hukumar INEC ya yi murabus
A wani rahoton, kun ji cewa shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ya ajiye aiki a ranar Talata, 7 ga Oktoban 2025.
Rahotanni sun bayyana cewa Farfesa Mahmood Yakubu ya ajiye aiki ne kafin wa'adinsa na shekara 5 ya karasa cika.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da ajiye aikin shugaban hukumar kuma an fara magana kan nada wanda zai gaje shi.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
