Labari Ya Fara Sauyawa: Malami Ya Fadi Shirin Ahlus Sunnah kan Zaben 2027 a Kano

Labari Ya Fara Sauyawa: Malami Ya Fadi Shirin Ahlus Sunnah kan Zaben 2027 a Kano

  • Maganar zargin da ake yi wa Sheikh Abubakar Lawan Triumph a Kano ta dauki sabon salo, yayin da gwamnatin jihar ta shiga cikin lamarin kai tsaye
  • Sheikh Ishaq Adam Ishaq ya bayyana cewa suna da shiri na musamman kan zaben 2027 domin su tabbatar da wanda zai tsaya tsayin daka wajen kare addini
  • Ya shawarci Ahlus Sunnah da su yanki katin zabe domin tabbatar da muradinsu, yana mai cewa su ne suka fi yawa a Kano da masallatai

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Maganar zargin Sheikh Abubakar Lawan Triump a Kano ta fara daukar wani sabon salo yayin da gwamnatin jihar ta shiga lamarin.

Wasu na ganin an saka siyasa a cikin lamarin wanda ke neman raba al'ummar Musulmi gida biyu game da zaben da ke tafe.

Kara karanta wannan

Yadda gwamnatin Abba ta shirya kashe N1.6bn don auren gata a jihar Kano

Sheikh ya ja kunnen Ahlus Sunnah kan zaben 2027a Kano
Sheikh Ishaq Adam Ishaq kenan yayin karatunsa a masallaci. Hoto: Sheikh Barr. Ishaq Adam Ishaq.
Source: Facebook

Shirin Ahlus Sunnah a Kano kan zaben 2027

Sheikh Ishaq Adam Ishaq ya yi magana a faifan bidiyo kan lamarin wanda shafin Abdullahin Gwandu TV ya wallafa a manhajar Facebook.

A cikin bidiyon, Malamin ya ce akwai shirin da suke yi game da zaben 2027 a Kano domin tabbatar da wanda zai kare addini.

Shehin malamin ya kuma shawarci dukan Ahlus Sunnah da su je su yanki katin zabe da kuma gyara ga wadanda na su ya samu matsala.

"Sakonmu na karshe, ba wasa muke ba, duk wanda ya san bai da kuri'a ya je ya samu ana bayarwa da sauran wadanda ta su ke da matsala.
"Ba wai za mu yi zabe ba ne kan APC ko PDP ko NNPP ko wani abu, ko a ina kake ka zauna a jam'iyyarka, romon dimukradiyya idan ya zo ka karbi kayanka.
"Amma dai akwai ajanda ta Sunnah cewa za mu nuna mutum daya, wanda shi za a zaba wanda za mu yi hakan ne domin ya kiyaye addini.

Kara karanta wannan

'Za a maimata June 12': Malami a Kaduna ya yi hasashe mai ban tsoro kan zaben 2027

- Sheikh Ishaq Adam Ishaq

Zargin Lawan Triumph ta fara daukar sabomn salo a Kano
Sheikh Ishaq Adam Ishaq da Malam Abubakar Lawan Triump. Hoto: Sheikh Barr. Ishaq Adam Ishaq, Malam Abubakar Shu'aib Lawan Triump.
Source: Facebook

Malamin ya bayyana yawan mabiyansu a Kano

Har ila yau, malamin ya ce ko tambaya aka yi an san su waye suka fi yawa a Kano inda ya ce ko masallatan Juma'arsu ma sun fi yawa.

Sheikh ya kuma bambance mambobinsu da sauran mabiya wasu akidu inda ya ce da ka ga mabiyansu za ka suna da hankali da ilimi.

Ya kara da cewa:

"Wannan shi ne abin da za mu yi, saboda wallahi idan da za a tambaya a Kano su waye suka fi yawa, waye za ka ce, mu Ahlus Sunnah mun fi yawa.
"Mafi yawan Ahlus Sunnah za ka gansu masu hankali ne, ba za ka ga mutum yana ihu a titi kamar mahaukaci ba."

Sheikh Ishaq ya fadi hukuncin da ya kamaci Turji

A baya, mun ba ku labarin cewa Sheikh Ishaq Adam Ishaq ya yi watsi da ra'ayin tattaunawar sulhu da ‘yan bindiga, yana mai cewa Musulunci ya umurci a yake su.

Kara karanta wannan

Triumph: An shawarci Abba game da kalaman mataimakinsa, Sagagi kan zargin taba annabi

Malamin ya bayyana cewa addini da dokar kasa duk sun amince a kashe su ko a hukunta su matukar suna ci gaba da barna.

Ya kalubalanci masu cewa ‘yan bindiga sun fi karfin jami’an tsaro, yana mai jaddada cewa gwamnati na da ikon kawo karshen su.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.