An Yi Baban Rashi: Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Sa'id Abubakar Ya Rasu a Kaduna

An Yi Baban Rashi: Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Sa'id Abubakar Ya Rasu a Kaduna

  • Babban limamin masallacin Juma'a na SMC da ke garin Kaduna, Sheikh Imam Sa'id Abubakar ya rasu da safiyar yau Alhamis, 2 ga Oktoba, 2025
  • Majalisar Limamai da Malamai ta jihar Kaduna ta tabbatar da rasuwar malamin a wata sanarwa da ta fitar, ta ce ya cika ne da asubah
  • Tuni dai aka yi jana'izar marigayin da misalin karfe 1:00 na rana bayan Sallar Azahar kamar yadda addinin musulunci ya tanada

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kaduna - Babban Malamin addinin Musulunci a jihar Kaduna da ke Arewacin Najeriya, Sheikh Imam Sa'id Abubakar ya riga mu gidan gaskiya.

Majalisar Limamai da Malamai ta jihar Kaduna ta tabbatar da rasuwar Imam Sa'id, ta ce ya rasu ne da Asubahin yau Alhamis, 2 ga watan Oktoba, 2025.

Sheikh Imam Sa'id Abubakar.
Hoton babban limamin masallacin SMC a Kaduna, Sheikh Imam Sa'id Abubakar. Hoto: Dr. Yusuf Yakubu Arrigasiyyu
Source: Facebook

An tabbatar da rasuwar Sheikh Sa'id Abubakar

Kara karanta wannan

Triumph: An shawarci Abba game da kalaman mataimakinsa, Sagagi kan zargin taba annabi

Sakataren Majalisar Limamai da Malamai ta Kaduna, Dr. Yusuf Yakubu Arrigasiyyu ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya wallafa shafinsa na Facebook.

Ya ce Marigayi Imam Sa'id Abubakar shi ne babban limamin masallacin Juma'a na Sardauna Memorial College watau SMC da ke Unguwan Dosa a cikin garin Kaduna.

Sanarwar ta ce:

"Inna lillahi wa inna Ilaihi Raji'un. Majlisar Limamai da Malamai na Jihar Kaduna na sanar da cewa Allah Ta'ala ya yi wa Shaikh Imam Sa'id Abubakar rasuwa.
''Marigayin, wanda shi ne babban limamin masallacin juma'a na SMC ya rasu da Asubah yau 10 ga watan Rabi'ul Thani, 1447AH wanda ya zo daidai da 2 ga watan Oktoba, 2025.
"Za'a yi jana'izar shi da karfe 1:00 na tsakar rana bayan Azahar in shaa Allahu. Allah Ya ji ƙan Imam Sa'id Abubakar."

Malamin ya sha fama da rashin lafiya

Bayanai daga Unguwan Dosa a Kaduna sun nuna cewa marigayin ya rasu ne bayan fama da doguwar jinya.

Tuni dai mabiya da sauran mutane suka fara tururuwar zuwa ta'aziyya da alhinin wannan babban rashi da suka yi.

Kara karanta wannan

Uwargidan Shugaban ƙasa, Remi Tinubu ta samu sarauta a Gombe

Wani mazaunin Kaduna, Isma'il Usman ya shaida wa Legit Hausa cewa rashin limaminbabban rashi ne ga musulunci, al'ummar Unguwar Dosa, Kaduna da ma Najeriya baki daya.

Imam Sa'id Abubakar.
Hoton marigayi Sheikh Sa'id Abubakar na masallacin SMC. Hoto: Isma'il Usman
Source: Facebook

Mutane sun yi jimamin rashin Imam Sa'id

Ya yi addu'ar Allah ya jikan malamin, Ya amshi kyawawan ayyukansa, kuma Ya sanya shi a gidan aljannah.

"Mun tashi da safiyar yau Alhamis da labarin rasuwar babban malami, Sheikh Sa'id Abubakar SMC (Babban Limamin Masallacin SMC Unguwan Dosa Kaduna."
"Ya rasu ne bayan doguwar jinya da ya yi, Allah Ka jikan Imam Sa'id SMC Ka sa Aljannace makoma, Sheikh Sa'id aminin mahaifina ne sosai," in ji shi.

Malaman darikan Tijjaniya 2 sun rasu

A wani labarin, kun ji cewa manyan malaman Darikar Tijjaniya guda biyu sun riga mu gidan gaskiya a Najeriya.

Malaman da suka rasu su ne Khalifan Tijjaniyya na Jihar Osun, Sheikh Abdul Kareem Raji, da Khalifan Tijjaniyya na Jihar Kwara, Sheikh Abubakar Siddeeq Agbade Abayawo.

Gwamna Ademola Adeleke, ya bayyana bakin cikinsa tare da mika sakon ta'aziyya bisa rasuwar wadannan manyan malamai na addinin musulunci guda biyu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262