"Mun Ceto Naira," Tinubu Ya Tabo Batun Darajar Kudin Najeriya a Jawabin Ranar 'Yanci

"Mun Ceto Naira," Tinubu Ya Tabo Batun Darajar Kudin Najeriya a Jawabin Ranar 'Yanci

  • Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa tsare-tsaren gwamnatinsa sun ceto Naira daga kalubalen da ta shiga a kasuwar canji
  • Shugaba Tinubu ya ce banbancin da aka rika samu a kasuwannin canji wanada ya kawo cin hanci, ya zama tarihi a yanzu
  • Mai Girma Shugaban ya ce farashin canjin Naira da Dalar Amurka ya daina dogaro da farashin danyen mai a kasuwar duniya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi ikirarin cewa kudin Najeriya watau Naira ta fita daga kalubale da rashin tabbas da ta shiga a shekarun baya.

Shugaba Tinubu ya ce matakan da gwamnatinsa ta dauka sun ceto Naira daga tangal-tangal da rashin tabbas a shekarun 2023 da 2024.

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.
Hoton Mai Girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnatin Najeriya. Hoto: @SundayDare
Source: Facebook

Bola Tinubu ya yi wannan furucin ne a jawabin ranar 'yancin kai da ya yi kai tsaye da yan Najeriya ranar Laraba, 1 ga watan Oktoba, 2025, cewar Premium Times.

Kara karanta wannan

Nigeria @65: Muhimman abubuwa 5 da Tinubu ya fada a jawabin ranar samun 'yanci

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bola Tinubu ya daidaita farashin Naira

Ya jaddada cewa Naira ta samu daidaito a kasuwar hada-hadar kudi ta bayan fage da wacce ke karkashin kulawar gwamnati.

"Tazarar farashin canji a kasuwar gwamnati da kasuwar bayan fage ya ragu matuka sakamakon sauye-sauyen da muka yi da karin zuba jari da shigowar kudin waje."
"Farashin canji mabanbanta da aka rika samu a baya wanda ya haifar da cin hanci da satar dukiyar kasa, yanzu ya zama tarihi.
"Bugu da kari, yanzu farashin canjin Naira da Dalar Amurka ya daina dogaro da farashin danyen mai a kasuwar duniya."

- Shugaba Bola Tinubu.

Halin da Naira ke ciki a kasuwar canji

A watannin baya-bayan nan, darajar Naira ta farfado musamman bayan samun karin kudaden da ’yan kasa ke turo wa daga ketare da kuma rage a gibin farashin canji a kasuwar gwamnati da ta bayan fage.

A wannan ahekarar da muke ciki, mafi munin faduwar darajar Naira shi ne lokacin da aka rika musayar kowace Dalar Amurka a kan N1,637.

Kara karanta wannan

Bayan wuya: Tinubu ya fadi yadda sauki ya fara samu wa Najeriya

A farkon makon nan, Naira ta kara mikewa yayin da Dalar Amurka ke faduwa. A kasuwar musayar kudaden waje ta Najeriya, farashin canji ya dawo ₦1,485.5/$.

Haka kuma, a kasuwar bayan fage, Naira ta dan karfafa a ranar Talata inda ta rufe a ₦1,500/$, sabanin ₦1,510/$ da aka yi musaya makon da ya gabata.

Dalar Amurka da Naira.
Hoton Dalar Amurka da takardun kudin Najeriya watau Naira. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Wane sauyi aka samu a darajar Naira?

Bisa wannan ne, Shugaba Tinubu ya tabbatar da cewa tsare-tsarensa sun farfado da darajar Naira ta hanyar samar da daidaiton farashi a kasuwannim canji.

Ya kuma bai wa yan Najeriya tabbacin cewa farashin canji ya daina dogaro da farashin danyen mai a duniya, cewar rahoton The Cable.

Tinubu ya kara kare kansa kan cire tallafi

A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa ta matakin tsige tallafin man fetur ne domin ceto tattalin arzikin Najeriya.

A jawabinsa na ranar cikar Najeriya shekaru 65 da samun yancin kai, Bola Tinubu ya ve cire tallafin fetur ba abu ne mai sauki ba amma ya zama wajibi.

Shugaban Kasar ya bayyana cewa ya gaji tattalin arzikin da ya kusa durkushewa, don haka dole ne a dauki tsauraran matakai.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262