Katsina: Mutane Sun Yi Kukan Kura, Sun Cafke Ƴan Bindiga da Ke Taimakon Bello Turji

Katsina: Mutane Sun Yi Kukan Kura, Sun Cafke Ƴan Bindiga da Ke Taimakon Bello Turji

  • Hare-haren yan bindiga sun kai mutane bango inda al'ummar wasu yankuna suka fara daukar mataki domin kawo karshen masifar
  • Mutanen Ƙadisau a karamar hukumar Faskari da ke jihar Katsina sun kama wasu da ake zargin yan bindiga ne
  • Daya daga cikin wadanda aka kama ya amsa cewa shi da kansa ya kashe mutane, yana safarar makamai ga Bello Turji

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Faskari, Katsina - Al’ummar Ƙadisau da ke Faskari a Jihar Katsina sun gaji da bala'in hare-haren yan bindiga a yankinsu.

Mutanen garin sun cafke mutane uku da ake zargi da hannu a kai hare-haren ’yan bindiga a yankin.

Mutane sun cafke yan bindiga 3 a Katsina
Gwamna Dikko Umaru Radda da Hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa. Hoto: Dikko Umaru Radda.
Source: Facebook

Rahoton Aminiya ya ce mutanen sun miƙa waɗanda suka kama ga jami’an tsaron al’umma domin gudanar da bincike kan wadansa aka cafken.

Kara karanta wannan

Asiri ya tonu: Dakarun sojoji sun cafke masu hada baki da 'yan ta'adda a Katsina

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda hare-haren yan bindiga ya kai mutane bango

Jihar Katsina na daga cikin jihohi da suka fi shan fama da hare-haren yan bindiga wanda ke jawo asarar rayuka da dukiyoyin al'umma.

Sauran jihohin Arewa da ke shan fama sun hada da Zamfara da Sokoto da Kaduna da kuma Niger a Arewa ta Tsakiyar Najeriya.

A baya bayan nan, mutane a Sokoto sun dauki doka a hannunsu inda suka yi gaba da gaba da yan ta'adda duba da zargin cewa jami'an tsaro sun gaza kare su daga cin kashi da ake yi musu.

Yadda dan bindiga ke taimakon Bello Turji

Majiyoyi sun tabbatar da cewa tuni jami'an tsaron suka fara yiwa yan bindigar da aka kama tambayoyi domin gano bayanai masu muhimmanci.

Wani daga cikin yan bindiga ya bayyana cewa shi ne ya kashe mutum a harin Ƙadisau saboda an gane shi a lokacin harin.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun shiga har gida sun datsa Sarkin Fulani da adda a Neja

Ya ƙara da cewa shi mai safarar makamai ne ga ’yan bindigar da Bello Turji ke jagoranta suka kai hari yankin Ƙadisau.

Dubun wasu yan bindiga ya cika a Katsina
Taswirar jihar Katsina da ke Arewa maso Yammacin Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Abin da yan bindigar ke cewa a Katsina

Na biyun ya amsa cewa shi ke safarar abinci, man fetur da kayayyaki zuwa ga wani rikakken dan bindiga mai suna Malam a daji.

Ya kuma bayyana cewa yana cikin wadanda suka kai hare-haren Wasani, Raudama da Unguwar Gizo inda mutane da dama aka kashe tare da sace wasu.

Na ukun kuma ya tabbatar da kai wa Malam kayan abinci, fetur da kayan gona, yana kuma hulɗa da wani jagora mai suna Auwali.

Bisa wannan, hukumomi suka ɗauki waɗannan mutane domin zurfafa bincike kan rawar da suka taka a kashe-kashe, sace-sace da safarar kaya.

Katsina: An kama masu taimakon yan bindiga

A baya, kun ji cewa dubun wasu masu hada baki da 'yan ta'adda ya cika bayan sun fada komar jami'an tsaro a jihar Katsina.

Dakarun sojoji tare da hadin gwiwar jami'an rundunar C-Watch sun samu nasarar cafke mutanen da ake zargi bayan gudanar da bincike.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai kazamin hari, an rasa rayukan jami'an tsaro a Kwara

Hakazalika, sojojin sun kuma samu nasarar ceto wani mutum da 'yan ta'adda suka dauke yana tsaka da aiki a gonarsa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.