Abin da Ya Sa Dole Gwamnonin Arewa Su Yi Magana da Murya Daya kan Matsalar Tsaro

Abin da Ya Sa Dole Gwamnonin Arewa Su Yi Magana da Murya Daya kan Matsalar Tsaro

  • Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya ce lokaci ya yi da gwamnonin Arewa za su hada kai wuri guda, su yi magana da murya daya
  • Dauda Lawal ya ce babu mai zuba hannun jarin da zai shigo ya zuba dukiyarsa a wurin da babu tsaro a Arewa
  • Ya ba da shawarar kulla wata yarjejeniya ko kafa kwamitin da zai rika magana da yawun jihohi 19 na Arewacin kasar nan

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bukaci gwamnonin jihohi 19 na Arewa su dunkule wuri daya, su rika magana da murya ɗaya kan harkokin tsaro da tattalin arziki.

Gwamna Dauda ya yi wannan kira ne a wurin taron zuba jari da farfado da harkokin masana'antun Arewa da aka gudanar a otal ɗin Abuja Continental.

Kara karanta wannan

Gwamna Abba Kabir ya aika da muhimmin sako ga jami'an gwamnatinsa

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara.
Hoton Gwamna Dauda Lawal a wurin taron da aka shirya kan Arewa a Abuja Hoto: @daudalawal
Source: Twitter

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa Dauda Lawal ne ya jagoranci zaman farko na taron, Channels tv ta ruwaito.

Ya bayyana cewa an shirya taron ne ta hannun Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ƙarƙashin jagorancin Farfesa Ango Abdullahi, inda aka haɗa duka manyan masu ruwa da tsaki daga Arewa baki ɗaya.

Gwamna Dauda ya ja hankalin 'yan Arewa

A jawabinsa, Gwamna Lawal ya yaba wa kungiyar saboda jajircewarta wajen ci gaba da fatan ganin Arewa ta magance matsalolin da suka addabe ta.

"Shirya wannan taron kadai ya nuna hangen nesan wannan kungiya duba da take da aka ba shi na, 'bude damarmakin da mu ke da su', kuma an zabi fannoni masu muhimmanci, ma'adanai, noma da lantarki.
"A Zamfara, mun san irin matsalar da muke fuskanta: ƙasa mai yalwar ma’adanai da filayen noma masu faɗi, amma mutanenmu ba su amfana da albarkatun ba.”

Kara karanta wannan

Gwamna Sule ya gayawa gwamnonin Arewa gaskiya kan rashin tsaro

“Tambayar da ke gabanmu a matsayin shugabanni ba wai me za a yi ba ne, amma ta yaya za mu haɗa kai mu sauya damar da muke da ita zuwa arziki? Dole mu ajiye komai, mu hada kanmu.

- Gwamna Dauda Lawal.

Abin da ya kamata gwamnonin Arewa su yi

Gwamna Lawal ya nanata cewa tsaro a Arewa shi ne kashin bayan zuba jari, yana mai jan hankalin gwamnonim jihohin Arewa 19 da su fifita hada kai fiye da siyasa.

A rahoton Daily Trust, Gwamna Dauda ya kara da cewa:

“Dole mu haɗa kai wajen tsare rayukan mutane da jawo masu zuba hannun jari. Tsaro shi ne tubalin farko na kowane ci gaba."
“Shawara ta ita ce ne mu kafa Northern Nigerian Economic Compact, wato wata yarjejeniya ta haɗin kai tsakanin jihohi 19 na Arewa domin yin magana da murya ɗaya kan harkokin tsaro da tattalin arziki."
Gwamna Dauda Lawal na Zamfara.
Hoton Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Gwamna Dauda ya ce babu maganar sulhu

A wani rahoton, kun ji cewa Gwamna Dauda Lawal ya sake nanata matsayarsa kan sulhu da 'yan ta'addar da ke kashe mutanen Zamfara ba dare ba rana.

Gwamna Dauda Lawal ya fadawa mutanen Zamfara cewa gwamnatinsa na nan a kan bakarta cewa ba za ta taba yin sulhu da 'yan bindiga ba.

Kara karanta wannan

Gwamna ya gwangwaje magidanta da tallafi bayan tsuntsaye da kwari sun tafka barna

Gwamnan ya ce a lokacin da yake shiga kauyukan, ya fahimci titunansu sun lalace don haka ya yi alkawarin gyara masu domin su ma su samu saukin zirga-zirga.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262