Matakan da Ake Bi wajen Nada Shugaban Hukumar Zabe ta INEC a Najeriya

Matakan da Ake Bi wajen Nada Shugaban Hukumar Zabe ta INEC a Najeriya

Yayin da wa'adin shugaban hukumar zaben Najeriya (INEC), Farfesa Mahmud Yakubu ya kusa karewa, an fara magana matakan da za a bi wajen maye gurbinsa.

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Wa'adin shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmud Yakubu zai kare a watan Nuwamban 2025.

Jam'iyyun siyasa da suka hada da APC, PDP da ADC da ma sauran 'yan kasa sun fara magana kan sabon shugaban INEC da za a nada.

Shugaba Tinubu da shugaban INEC, Farfesa Mahmud Yakubu
Shugaba Tinubu da shugaban INEC, Farfesa Mahmud Yakubu. Hoto: INEC Nigeria|Bayo Onanuga
Source: Facebook

A wannan rahoton, mun tattaro muku hanyoyi ko matakan da ake bi wajen nada shugaban hukumar zabe a Najeriya.

1. Shugaban kasa zai sabi shugaban INEC

Shafin Law Global Hub ya wallafa cewa sashe na 153 na kundin tsarin mulkin Najeriya ya samar da matakan da ake bi wajen nada shugaban INEC.

Kara karanta wannan

Hankalin Tinubu ya koma kan kundin tsarin mulki, yana so a yi masa kwaskwarima

Sashen ya ce akwai manyan kwamishinoni da majalisu na tarayya 14 da doka ta amince da su, ciki har da majalisar shari’a ta kasa, majalisar kasa da kuma INEC.

Sashe na 154 ya yi karin bayani kan cewa shugaban kasa ne zai zabi wanda ya ke so ya zamo shugaban INEC.

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu yana jawabi
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu yana jawabi. Hoto: Bayo Onanuga
Source: Twitter

Ga abin da kundin tsarin mulki ya ce a sakin layi na 3:

“A yayin da shugaban kasa zai yi amfani da ikonsa na nada mutum a matsayin shugaban ko memba na Hukumar Zabe ta Kasa mai zaman kanta (INEC), ko Majalisar Shari’a ta Kasa,
"Ko kuma Hukumar Kidayar Jama’a ta Kasa, shugaban kasa zai tuntubi majalisar kolin kasa.”

Sai dai duk da haka, jaridar Punch ta wallafa cewa dole wanda shugaban kasar zai nada ya zamo ya kai shekara 50 da haihuwa ko sama da haka kuma mai nagarta.

2. Tuntubar majalisar kolin kasa

Business Day ta wallafa cewa kundin tsarin mulkin ya yi tanadi da cewa shugaban kasar zai yi shawara da majalisar kolin kasa kafin nada shugaban INEC.

Mambobin majalisar kolin kasa sun ƙunshi shugaban kasa wanda shi ne shugaban majalisar; mataimakin shugaban kasa, wanda shi ne mataimakin shugabanta.

Kara karanta wannan

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mahmood Yakubu a shugabancin INEC

Haka zilika akwai dukkan tsofaffin shugabannin kasa, dukkan tsofaffin alkalan kasa, shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai.

Marigayi Buhari da wasu shugabanni a wani taron majalisar kasa
Marigayi Buhari da wasu tsofaffin shugabanni a wani taron majalisar kasa. Hoto: Bashir Ahmad
Source: Twitter

Baya ga haka akwai dukkan gwamnonin jihohin Najeriya da kuma babban lauyan gwamnatin tarayya.

3. Za a tantance shugaban INEC a majalisa

Bayan shugaban ƙasa ya zaɓi wanda yake so ya naɗa, bayan tuntubar majalisar ƙasa, sai a gabatar da sunan wanda aka zaba ga majalisar dattawa domin tantancewa.

Ba za a tabbatar da shi ba sai idan ya tsallake tantancewa a majalisa. Tantancewar na iya zama mai tsauri domin tabbatar da nagartar wanda shugaban kasa ya zaba.

Wani sashe na majalisar dattawa yayin zaman da suka yi a Abuja
Wani sashe na majalisar dattawa yayin zaman da suka yi a Abuja. Hoto: Nigerian Senate
Source: Facebook

Da zarar an tantance wanda aka tura sunan shi majalisa, shugaban kasa zai sanar da nada shi ba tare da bin wasu matakai ba kamar jin ra'ayin yan kasa.

Shugaban hukumar zai yi wa'adi daya mai shekara biyar a bisa kundin tsarin mulki, daga nan kuma shugaban kasa na da ikon sake nada shi ko ya zabi wani.

An yi gargadi kan nada shugaban INEC

A wani rahoton, kun ji cewa kusa a jam'iyyar NNPP, Buba Galadima ya yi gargadi kan shugaban INEC da za a nada a Najeriya.

Kara karanta wannan

APC, ADC da PDP sun 'ayyana' wanda suke fata Tinubu ya ba shugaban INEC

Buba Galadima ya yi ikirarin cewa shugaban kasa na shirin nada wani tsohon alkali a matsayin wanda zai maye gurbin Farfesa Mahmud Yakubu.

Ya kara da cewa idan har Bola Tinubu ya nada mutumin da ake hasashe, za a iya yakin basasa a Najeriya saboda abubuwan da za su biyo baya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng