Abinci Ya Kare: Gwamna Ya Kori Wasu Manyan Jami'an Gwamnati 2 daga Aiki

Abinci Ya Kare: Gwamna Ya Kori Wasu Manyan Jami'an Gwamnati 2 daga Aiki

  • Gwamnatin Bauchi karkashin jagorancin Gwamna Bala Mohammed ta gano wasu manyan jami'ai biyu da ke amfani da takardun bogi
  • Hukumar Kula da Ma'aikatan Gwamnati a Bauchi ta kori jami'an daga aiki a wani bangare na tsaftace harkokin aikin gwamnati
  • Bayan haka, hukumar ta kara wa wasu ma'aikata girma ciki har da daraktoci da mataimakansu, da wasu lauyoyin gwamnati

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Bauchi - Gwamnatin Jihar Bauchi karkashin Gwamna Bala Mohammed ta kori wasu manyan ma’aikata biyu saboda amfani da jabun takardu.

Wadanda abin ya shafa sun hada da Yusuf Adamu Ningi, jami’in gudanarwa, da kuma Suleiman Ahmed (Ahuta), wadanda aka tura su zuwa Fadar Gwamnatin Bauchi.

Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi.
Hoton gwamnan jihar Bauchi, Santa Bala Mohammed Hoto: @SenBalaMohammed
Source: Facebook

Hukumar Kula da Ma'aikatan Gwamnatin Bauchi ce ta sanar da korar wadannan manyan jami'ai a wata sanarwa da mai magana da yawunta, Saleh Umar ya fitar yau Laraba, in ji Leadership.

Kara karanta wannan

'Dan majalisa Gabdi ya ce gwamnoni ne matsalar kasar nan, ya ba talakawa shawara

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bayyana cewa an dauki wannan mataki ne a taron da hukumar ta gudanar jiya Talata a Bauchi.

Dalilin korar manyan jami'ai 2 a Bauchi

Sanarwar ta ce bincike ya tabbatar da cewa jami’an sun aikata laifin amfani da jabun takardu, wanda ya saba da dokokin aikin gwamnati na jihar (Rule 0327 ii, iii da vi).

Saleh Umar ya ce hukuncin korar ya fara aiki ne daga ranar 23 ga Satumba, 2025, cewar rahoton Daily Post.

A wani bangare na taron, hukumar kula da ma'aikatan Bauchi ta amince da kara wa wasu daraktoci uku girma zuwa mukamin manyan daraktoci.

Sannan kuma ta tabbatar da daga matsayin mataimakan daraktoci hudu zuwa matsayin daraktoci.

An kara wa wasu ma'aikata girma

Wadanda suka samu karin girma sun hada da daraktoci na gudanarwa da albarkatun dan Adam, daraktan bincike da lissafi, da kuma daraktocin tsare-tsare, shari’a da harkokin kasa da kididdiga.

Kara karanta wannan

Sanata Barau ya bi sahun Gwamna Abba, ya tura dalibai 1000 karatu a jami'ar Katsina

Haka kuma, hukumar ta amince da daukaka matsayin wasu lauyoyi guda takwas da babban jami’in kula da filaye zuwa matsayin mataimakin darakta, da sauransu.

Shugaban hukumar ma'aikatan Bauchi, Dr. Ibrahim Alhaji Muhammad, ya yi kira ga ma’aikatan gwamnati da su rika bin doka da ka’idojin aiki yadda ya kamata.

Ya jaddada cewa hakan zai kawar da ayyukan da suka sabawa doka, ya kara masu mutunci, kuma ya inganta aikin gwamnati tare da kawar da cin hanci da rashawa ba.

Gwamna Bala Mohammed.
Hoton gwamnan Bauchi, Bala Mohammed a fadar gwamnatinsa Hoto: Sen. Bala Mohammed
Source: Twitter

Gwamnatin Bauchi ta taya ma'aikata murna

Yayin da ya taya wadanda aka karawa girma murna, Dr. Ibrahim ya nanata kudirin hukumar na ba sani ba sabo kan duk wanda ya kuskura ya aikata barna.

Ya ce hukumar za ta ci gaba da kokarin tabbatar da ladabi, bin doka, da gaskiya a dukkan bangarorin aikin gwamnati na jihar Bauchi.

Bauchi: Gwamnatin ta gano ma'aikatan bogi

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin jihar Bauchi ta tabbatar da cewa ta gano ma’aikatan bogi sama da 100 a bangaren lafiya.

Shugaban hukumar kula da asibitocin jihar, Malam Sambo Alkali, ya ce an gano wadannan ma'aikata na bogi ne a binciken da aka gudanar a bincike wasu cibiyoyin lafiya guda biyar.

Kara karanta wannan

Gwamnan Kano ya yi garambawul a gwamnatinsa, kwamishinoni 2 za su mika mulki yau

Malam Sambo Alkali ya kuma tabbatar da cewa duka wadanda aka gano za su fuskanci hukunci daidai da abin da suka aikata.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262