'Yan Bindiga Sun Kai Hari a Zamfara, an Yi Awon Gaba da Mutane Masu Yawa

'Yan Bindiga Sun Kai Hari a Zamfara, an Yi Awon Gaba da Mutane Masu Yawa

  • An shiga jimami a jihar Zamfara bayan wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun farmaki mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba
  • Tsagerun 'yan bindigan sun kai farmakin ta'addancin ne a wani kauye da ke karamar hukumar Bungudu
  • Harin na 'yan bindigan ya jawo an raunata wasu mutum uku tare da yin awon gaba da mutane masu yawa zuwa cikin daji

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Zamfara - Ƴan bindiga dauke da makamai sun kai farmaki a karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara.

'Yan bindigan sun kai harin ne a kauyen Bayan Dutsi da ke yankin Tofa, a karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara.

'Yan bindiga sun kai hari a Zamfara
Hoton gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a shafinsa na X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Yan bindiga sun yi ta'asa a Zamfara

Kara karanta wannan

Sojoji sun gwabza kazamin fada da 'yan bindiga, an samu asarar rayuka

A yayin harin, 'yan bindigan sun raunata mutane uku tare da sace wasu da ba a tantance adadinsu ba.

Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:15 na dare a ranar Litinin, 22 ga Satumban 2025.

'Yan bindigan sun kutsa kauyen ne suna harbe-harbe kan mai uwa da wabi, lamarin da ya jawo raunuka ga wasu mazauna yankin tare da yin garkuwa da wasu.

"Bayan samun rahoton gaggawa, dakarun haɗin gwiwa na Operation Fansa da jami'an rundunar Askarawan Zamfara sun garzaya zuwa yankin."
"An garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibiti domin kula da lafiyarsu."

- Wata majiya

Jami'an tsaro sun tsaurara matakan kariya

Haka kuma, majiyoyin sun bayyana cewa jami’an tsaro sun kara ninka kokarin da suke yi domin ceto mutanen da aka sace da kuma dawo da zaman lafiya a yankin da lamarin ya shafa.

Hare-haren 'yan bindiga sun zama ruwan dare a jihar Zamfara, inda tsagerun suke cin karensu babu babbaka.

Mutane da dama sun rasa rayukansu yayin da wasu suka rasa matsugunansu sakamakon hare-haren na 'yan bindiga.

Kara karanta wannan

Matsala ta girma: An gano gawarwakin yan sanda 8 bayan sun bace a Najeriya

Ko a cikin 'yan kwanakin nan, sai da 'yan bindiga suka yi awon gaba da mutum 18 da suka hada da mata da yara a wani hari da suka kai a Zamfara.

'Yan bindiga sun kai harin ta'addanci a Zamfara
Taswirar jihar Zamfara, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Karanta wasu karin labaran kan 'yan bindiga

Sojoji sun fafata da 'yan bindiga

A wani labarin kuma, kun ji cewa dakarun sojojin Najeriya sun yi arangama mai zafi da 'yan bindiga a jihar Neja.

Sojojin tare da hadin gwiwar 'yan sa-kai sun fafata da 'yan bindigan ne a wani kauye da ke karamar hukumar Mariga.

Dakarun sojojin sun nuna bajinta yayin artabun, inda suka hallaka 'yan bindiga masu tarin yawa tare da kubutar da fararen hula.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng