An Shiga Fargaba bayan Ɓacewar Hadimin Gwamna a Hanyarsa Ta Zuwa Abuja

An Shiga Fargaba bayan Ɓacewar Hadimin Gwamna a Hanyarsa Ta Zuwa Abuja

  • Al’umma a Benue sun shiga fargaba bayan bacewar mutum biyu ciki har da Atu Terver, hadimin Gwamnan jihar a kan harkokin matasa
  • Matarsa, Chivir Terver, ta tabbatar mijinta ya tashi daga Makurdi zuwa Abuja amma bai isa ba, lamarin da ya jefa iyalinsu cikin damuwa
  • Rundunar ’yan sanda ta ce ba ta da masaniya kan cafke Asom Jerry, kuma bacewar Terver ta auku ne a birnin Abuja, ba a Benue ba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Makurdi, Benue - Al'ummar jihar Benue sun shiga fargaba bayan bacewar mutane biyu daga jihar da aka rasa sama ko kasa.

Fargaba ta mamaye jama’a bayan bacewar wasu matasa biyu, ciki har da wani hadimin Gwamna Hyacinth Alia mai suna Atu Terver.

Hadimin gwamna ya bata ya hanyarsa ta zuwa Abuja
Gwamna Alia Hyacinth na jihar Benue. Hoto: Fr. Alia Iormen Hyacinth.
Source: Facebook

An gano cewa Terver shi ne hadimin gwamna na musamman kan sha'anin matasa da yada labarai, inda aka ce ya bace a hanyarsa ta Makurdi zuwa Abuja, cewar Leadership.

Kara karanta wannan

Kwana ya kare: Malamin da ya fi 'tsufa' yana wa'azi ya bar duniya yana shekaru 95

Yadda yan bindiga suka addabi jihar Benue

Wannan batan matasa biyu a Benue na zuwa ne yayin da jihar ke fama da matsalar tsaro na hare-haren yan bindiga a wasu yankuna.

Lamarin bai ba da mamaki ba yayin da ake zargin batan na da nasaba da ayyukan yan bindiga da suka addabi jihar da yankin Arewa ta Tsakiyar Najeriya.

Al'ummar na ci gaba fatan samun matasan cikin koshin lafiya da kira ga gwamnati da ta yi gaggawar daukar mataki kan lamarin.

An rasa matashi dan gwagwarmaya a Benue

Haka kuma, Asom Jerry wani mai fafutuka a kafafen sada zumunta ya bace, lamarin da ya tayar da cece-kuce, wasu na cewa ’yan sanda sun cafke shi.

Matar hadimin gwamna, Chivir Terver, ta tabbatar da cewa mijinta ya bar Makurdi zuwa Abuja ranar Talata 16 ga watan Satumbar 2025 amma bai isa gare su ba.

Kara karanta wannan

A karshe, Shugaba Tinubu ya cire dokar ta bacin da ya sanya a jihar Ribas

Ta ce:

“Ya tafi daga Makurdi ranar Talata zuwa Abuja, amma bai zo gare mu ba. Mun kai korafi ofishin ’yan sanda, suna bincike har yanzu.”
Ana neman matashi da hadimin gwamna bayan sun bata a Benue
Taswirar jihar Benue da ke Arewa ta Tsakiyar Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Menene rundunar 'yan sanda ta ce?

Jami’ar hulda da jama’a ta ’yan sanda, Udeme Edet, ta ce ba ta da masaniya kan cafke Jerry da kuma bacewar Terver ta faru ne a Abuja.

Ta kara da cewa tana jin labarin ne daga manema labarai kawai, sannan ta jaddada cewa lamarin ya faru a Abuja, ba a jihar Benue ba.

Edet ta tabbatar da cewa duk lokacin da labarin ya iso ta, za ta yi ƙarin bayani kan lamarin ba tare da bata lokaci ba, cewar Daily Post.

'Yan bindiga sun hallaka bayin Allah a Benue

Mun ba ku labarin cewa an samu asarar rayuka a jihar Benue bayan wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai hari a wani kauye.

'Yan bindigan sun kai harin ne a wani kauye dake karamar hukumar Ogbadibo inda suka bude wuta kan mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Ƴan bindiga sun sace ƴar NYSC da ɗalibar jami'a, suna neman N50m

Mummunan harin da 'yan bindigan suka kai ya jawo asarar rayuka da raunata wani matashi wanda hakan ya tilasta aka garzaya da shi zuwa asibiti.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.