Katsina: Bayan Kachallah Isiya, Tantirin Dan Bindiga Ya Cika Alkawari domin Mutunta Sulhu

Katsina: Bayan Kachallah Isiya, Tantirin Dan Bindiga Ya Cika Alkawari domin Mutunta Sulhu

  • Maganar sulhu da yan bindiga don zaman lafiya na ci gaba da sauya salo a wasu yankunan jihar Katsina
  • An gudanar da zaman sulhu a kwanan nan a karamar hukumar Faskari da dan bindiga, Ado Aliero
  • Wasu daga cikin wadanda aka yi sulhu da su sun fara sakin mutanen da ke hannunsu saboda mutunta tsarin

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Katsina - Da alamu zaman sulhu da aka yi a wasu yankunan jihar Katsina na haifar da ɗa mai ido yayin aka fara sakin jama'a.

Wasu yankunan jihar sun yi zama na musamman da yan bindiga domin tabbatar da samun zaman lafiya.

Dan bindiga ya sake mata bayan zaman sulhu
Mata da dan bindiga ya sake a Katsina bayan sulhu. Hoto: @ZagazOlamakama.
Source: Twitter

Rahoton Zagazola Makama ya tabbatar da cewa wasu yan bindiga sun fara sakin mutanen da suka yi garkuwa da su.

Kara karanta wannan

Jagoran 'yan bindiga ya fara cika alkawari kan yarjejeniyar sulhu a Katsina

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Katsina: Yadda dan bindiga ya fara sakin mutane

Yarjejeniyar sulhun da aka cimmawa a karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina ta fara aiki bayan hobbasa daga wasu yan bindiga.

Hakan ya biyo bayan fara cika alkawura da yan bindiga suka fara yi daga bangaresu saboda zaman sulhu da aka yi.

Jagoran 'yan bindiga, Isiya Akwashi Garwa, ya mutunta batun sulhu ta hanyar sako mutanen da ya yi garkuwa da su.

Mazauna yankin sun nuna farin cikinsu kan wannan lamari, inda su ka bukaci ya yi wa sauran miyagu magana su daina kai hare-hare.

Ana ci gaba da sake mutane bayan sulhu da yan bindiga a Katsina
Taswirar jihar Katsina da ke Arewa maso Yamma a Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Wani dan bindiga ya cika ka'aida

Wani hatsabibin dan bindiga da ya tuba ya saki wasu mutane da ya kama domin a biya shi kudin fansa kafin zaman sulhu da aka yi.

Dan bindigar ya saki mata har guda uku a jihar Katsina a matsayin wani bangare na tsarin zaman lafiya wanda yanzu ake kokarin samarwa a Katsina.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da maganar sulhu, Ado Aliero ya yi wa Sarki yankan rago a Zamfara

Matan, wadanda ba a bayyana sunayensu ba, an ce sun kwashe lokaci a hannun Kacallah Zailani, fitacce ’dan bindiga a Maigora.

Majiyoyi daga al’umma sun shaida cewa a ranar Laraba 17 ga watan Satumbar 2025 cewa Zailani ya sake su ba tare da an biya kudin fansa ba.

“Ya mika matan ga masu sasanci a matsayin alamar kyakkyawan niyya don tabbatar da yarjejeniyar zaman lafiya."

- In ji wata majiya

Yadda mutane ke kallon sulhu da yan bindiga

Mutane da dama na damuwa kan sakin mutane da yan bindiga suke yi inda mafi yawa ke fargaba komai na iya faruwa saboda ba su da amana.

Duk da haka wasu bangare na ganin sulhu shi ne kawai hanyar samun zaman lafiya ciki har da malaman addini kamar Sheikh Musa Yusuf Assadus Sunnah.

Yaran Aliero sun yanka Sarki a Zamfara

Mun ba ku labarin cewa yan bindiga da Ado Allero ke jagoranta sun kawo tsaiko yayin da ake cikin maganar sulhu da yan bindiga a Katsina.

Gungun miyagun karkashin Aliero sun kashe Hakimin Dogon Dawa a Keta, Tsafe Zamfara, tare da sace mutane 40 a masallaci.

Kara karanta wannan

Sa'o'i da sulhu, 'yan bindiga sun rufe masallaci, sun sace masu sallah 40 da Asuba

Duk da sulhun da ake yi a Faskari, hare-haren sun ci gaba da faruwa, ciki har da sace mutane 12 a Bukuyum da 4 a Tudun Moriki.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.