Manyan Jagororin 'Yan Ta'adda da Aka Gani wajen Zaman Sulhu a Katsina

Manyan Jagororin 'Yan Ta'adda da Aka Gani wajen Zaman Sulhu a Katsina

Jihar Katsina - An gudanar da wani taron zaman sulhu da 'yan ta'adda a jihar Katsina don samun zaman lafiya.

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Taron zaman sulhun dai ya gudana ne a kauyen Hayin Gada da ke karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina.

Jagororin 'yan ta'adda sun je zaman sulhu a Katsina
Hotunan jagororin 'yan ta'adda Ado Aleiro, Kachallah Babaro da Isiya Kwashen Garwa Hoto: @ZagazolaMakama
Source: Twitter

An yi zaman sulhu da 'yan ta'adda a Katsina

Masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya kawo rahoto kan zaman sulhun.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taron zaman sulhun ya samu halartar shugabannin al’umma, wakilan jami'an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki.

A wajen taron, an jaddada bukatar nuna gaskiya da jajircewa don kawo karshen ta’addanci a yankin.

Taron wanda aka bayyana a matsayin irinsa mafi girma, ya haɗa gungun kungiyoyin 'yan bindiga da dama da su ka sha alwashin rungumar zaman lafiya da zama tare da al’umma.

Kara karanta wannan

An nuna fuskar Kachalla Babaro da ya kai hari masallaci, ya kashe Musulmai

Ra’ayoyi sun bambanta kan sulhu

Wasu mutane dai na kallon batun sulhun a matsayin wata dama ta dawo da zaman lafiya.

Yayin da wasu kuma ke shakku kan gaskiyar 'yan ta'addan duba da irin muggan ayyukan da su ka aikata a baya.

Jagororin 'yan ta'adda da su ka halarci zaman sulhu

Taron zaman sulhun ya samu halartar manyan jagororin 'yan ta'adda daga ciki da wajen jihar Katsina.

Ga jerinsu a nan kasa:

1. Ado Aleiro

Hatsabibin jagoran 'yan ta'adda, Ado Aleiro, na daga cikin mutanen da aka gani a wajen zaman sulhu.

Ado Aleiro na daga cikin mutanen da su ka gabatar da jawabi a wajen taron wanda aka gudanar a karamar hukumar Faskari.

Jagoran 'yan ta'addan ya nuna fatan cewa za a samu zaman lafiya a Katsina da ma sauran wurare bayan zaman tattaunawar.

A cikin jawabinsa, Ado Aleiro ya tuna irin gudummawar da ya bayar a baya a shirin zaman lafiya, inda ya bayyana cewa an rushe tsarin ne bayan cafke ɗansa.

Kara karanta wannan

Jagoran 'yan bindiga, Ado Aliero ya mika wuya ga zaman lafiya bayan sulhu

Jagoran 'yan ta'addan ya ce sabuwar tattaunawar nada matukar muhimmanci domin a karon farko an ga tarin manyan 'yan bindiga sun fito fili.

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa sakamakon taron zai tabbatar da zaman lafiya, ba kawai a Faskari ba har ma a kasar baki ɗaya.

2. Isiya Kwashen Garwa

Jagoran 'yan ta'adda, Isiya Kwashen Garwa, na daga cikin mutanen da suka halarci zaman sulhun.

A baya Hedikwatar Tsaro ta kasa ta ayyana shi a cikin jerin 'yan ta'addan da ake nema ruwa a jallo.

Akwai sunan Isiya Kwashen Garwa, a cikin jerin manyan ƴan ta’adda da ƴan bindiga 19 da ake nema a Najeriya.

Isiya Kwashen Garwa, dan aalin kauyen Kamfanin Daudawa ne na karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina.

An daɗe ana danganta shi da kashe-kashe, sace-sace da kai hare-hare a dazukan jihar Katsina da sauran jihohi makwabta.

Shafin Katsina Daily News ya sanya bidiyon jawabin da jagoran 'yan ta'addan ya yi a wajen taron.

A cikin jawabinsa, ya bayyana cewa sun dauki makamai ne don rama muzgunawar da ake yi wa 'yan uwansu Fulani.

Kara karanta wannan

Sojoji sun kashe jagoran 'yan ta'adda, Kachalla Babangida bayan gumurzu

Ya rika jawo ayoyin Al-Kur'ani mai girma don karin gaske kan bayanan da ya rika yi a wajen taron.

3. Kachallah Babaro

Jagoran 'yan ta'adda Kachallah Babaro ya bayyana a wajen zaman sulhun da aka yi a jihar Katsina.

Kachallah Babaro ya halarci zaman sulhu a Katsina
Hoton jagoran 'yan ta'adda, Kachallah Babaro Hoto: Zagazola Makama
Source: Facebook

Hatsabibin dan ta'addan ya daɗe yana addabar yankin kananan hukumomin Kankara da Malumfashi na jihar Katsina.

Rahotanni sun nuna shi ne ya kai mummunan harin da ya hallaka masallata 32 a kauyen Mantau karamar hukumar Malumfashi.

4. Hassan Dan Tawaye

Hatsabibin jagoran 'yan ta'adda, Hassan Dan Tawaye, na daga cikin mutanen da aka gani wajen zaman sulhu a karamar hukumar Faskari.

Jagoran 'yan ta'aadan ga halarci zaman ne don ganin an samu zaman lafiya a yankin tare da daina kai hare-hare.

A jawabin da ya yi, ya nuna muhimmancin zaman lafiya tsakanin al'ummar Hausa-Fulani.

Sojoji sun ragargaji 'yan ta'adda

A wani labarin kuma, kun ji cewa dakarun rundunar sojojin Najeriya, sun ragargaji 'yan ta'adda a jihar Katsina.

Dakarun sojojin sun yi artabun ne da 'yan ta'adda a karamar hukumar Kankara, inda aka yi nasarar hallaka miyagu guda 23.

Kara karanta wannan

An bankado abubuwa, matar shedanin 'dan bindiga ta shiga hannu a Zamfara, ta tsure

Dakarun sojojin sun kuma samu nasarar ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, wadanda suka hada da mata da kananan yara daga hannun tantiran.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng