An Zo wajen: Gwamna Dauda Ya Yi Fallasa kan Matsalar 'Yan Bindiga a Zamfara

An Zo wajen: Gwamna Dauda Ya Yi Fallasa kan Matsalar 'Yan Bindiga a Zamfara

  • Gwamnan jihar Zamfara ya fito ya yi magana kan matsalolin da ke kawo cikas a yakin da ake yi da 'yan bindiga
  • Dauda Lawal ya bayyana cewa an kasa kawo karshen matsalar ne saboda abubuwan da suka fi karfin ikonsa
  • Gwamnan ya nuna cewa duk da matsalolin da ake samu, yana bakin kokarinsa wajen ganin ya sauke nauyin da ke kansa na kare mutanen Zamfara

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Zamfara - Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi magana kan matsalar 'yan bindiga da ake fama da ita.

Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa yana sane da ainihin wuraren da manyan shugabannin ‘yan bindigan da ke addabar jihar suke.

Gwamna Dauda ya ce ya san inda 'yan bindiga suke a Zamfara
Hoton gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Jaridar Leadership ta ambato gwamnan na cewa ba shi da ikon daukar mataki ne saboda ba shi ne ke da iko kan hukumomin tsaro ba.

Kara karanta wannan

Minista ya fadi yadda manufofin Tinubu su ka ceto albashin ma'aikata a jihohi 27

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Dauda ya tabo batun 'yan bindiga

Gwamna Dauda Lawal ya koka kan yadda yaki da 'yan bindiga yake kwan gaba kwan baya a jihar.

Ya bayyana cewa duk da sanin motsin ‘yan bindiga, an kasa shawo kana matsalar ne saboda shugabannin tsaro a Zamfara suna karɓar umarni ne kawai daga Abuja.

Gwamnan ya bayyana cewa yana da masaniya kan duk inda shugabannin 'yan bindiga suke a jihar, amma ba zai iya yi musu komai ba.

Ya nuna cewa ko fita suka yi zai sani amma ba yadda ya iya da su tun bai da iko kan hukumomin tsaro.

Gwamnan ya bayyana cewa hakan ya kan sanya ya zubar da hawaye, saboda ga matsala yana gani amma bai da ikon kawo karshenta, rahoton The Punch ya tabbatar.

“Na rantse da Allah Maɗaukaki, duk inda shugaban ‘yan bindiga yake a cikin Zamfara, na sani, kuma idan ya fita, na sani."

Kara karanta wannan

'Abin da ya hana ni daƙile matsalar tsaro cikin mako 2 a Zamfara,' Dauda ya koka

- Gwamna Dauda Lawal

Gwamna Dauda ya bada misali kan yadda ‘yan bindiga suka taba kai hari a karamar hukumar Shinkafi, amma jami’an tsaro a jihar suka ki tunkararsu saboda ba su samu izini daga Abuja ba.

"Akwai lokacin da ‘yan bindiga suka kutsa Shinkafi, aka sanar da jami’an tsaro, amma suka ki fita saboda kawai ba a basu umarni daga Abuja ba."

- Gwamna Dauda Lawal

Gwamna Dauda Lawal ya koka kan rashin tsaro
Hoton gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, wajen kaddamar da rundunar CPG Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Wane mataki Gwamna Dauda ke dauka?

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ta yi duk mai yiwuwa don tallafa wa hukumomin tsaro duk da cewa ba shi da ikon shugabanci a kansu kai tsaye.

"Ina yin hakan ne duk da cewa ba ni da iko a kan hukumomin tsaro, amma saboda nauyin da ke kaina na kare rayuka da dukiyoyin jama’ar Zamfara."

- Gwamna Dauda Lawal

Mutanen gari sun yi fito na fito da 'yan bindiga

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu mutanen gari a jihar Sokoto sun yi arangama da 'yan bindiga.

Kara karanta wannan

Tinubu ya amsa kira kan kirkirar 'yan sandan jihohi, ya gano sirrin magance ta'addanci

Mutanen sun nuna jarumta inda suka shiga cikin daji suka fafata da 'yan bindiga bayan sun yi awon gaba da wasu bayin Allah.

Artabun da suka yi, ya sanya sun samu nasarar ceto mutanen da aka sace tare da hallaka wasu daga cikin 'yan bindigan.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng