Harin Masallaci: Gwamna Radda Ya Ziyarci Kauyen Mantau, Ya Dauki Alkawura

Harin Masallaci: Gwamna Radda Ya Ziyarci Kauyen Mantau, Ya Dauki Alkawura

  • Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya kadu kan mummunan harin da 'yan bindiga suka kai a karamar hukuma Malumfashi
  • Malam Dikko Umaru Radda PhD ya ziyarci kauyen domin yin ta'aziyya tare da jajantawa iyalan wadanda lamarin ya ritsa da su
  • A yayin ziyarar gani da ido da ya kai kauyen, Gwamna Radda ya dauki alkawura domin saukaka radadin da mutanen yankin suke ciki

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Katsina - Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya kai ziyarar ta’aziyya zuwa kauyen Mantau a karamar hukumar Malumfashi.

Gwamna Radda ya ziyarci kauyen bayan da ’yan bindiga suka kashe masallata 32 lokacin da suke Sallah a masallaci.

Gwamna Radda ya je jaje kauyen Mantau
Gwamna Dikko Radda yayin ziyarar da ya kai kauyen Mantau a Katsina Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Hakan na kunshe ne a cikin wata wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamna, Ibrahim Kaulaha Mohammed, ya sanya a shafinsa na Facebook, ranar Laraba, 27 ga watan Agustan 2025.

Kara karanta wannan

China ta ba da tallafin ambaliya, za a raba Naira biliyan 1.5 a jihohin Arewa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Harin 'yan bindiga ya sosa zuciyar gwamna Radda

Gwamna Radda a yayin ziyarar tasa ya sanar da bayar da tallafin gaggawa na N500,000 ga kowane gida da lamarin ya shafa.

Ya nuna takaici matuka kan mummunan harin tare da kira ga al’umma da su haɗa kai wajen yaki da rashin tsaro.

"Abin da na gani abin taɓa zuciya ne, marayu, gidaje da aka kona, da iyalai cikin tashin hankali. Mun tambaye su bukatunsu, na kuma tabbatar musu cewa gwamnati za ta magance waɗannan matsaloli ɗaya bayan ɗaya."

- Gwamna Dikko Radda

Me Gwamna Radda ya ce kan harin Mantau

Ya bayyana cewa an kai harin ne a matsayin ramuwar gayya bayan mazauna ƙauyen sun kori ’yan bindigan a baya, inda suka kashe guda bakwai tare da kwace makamai.

A cewarsa, an kashe mutane 32, mutum 20 a cikin masallaci da mutum 12 a wajen masallacin.

Sannan gwamnan ya ce an kona gidaje 20 tare da yin garkuwa da mutane 76, duk da dakarun sojojin saman Najeriya sun kubutar da su washegari.

Kara karanta wannan

"Na hakura": Gwamna Bala ya bayyana dalilin jingine burin yin takarar shugaban kasa

Gwamna Radda ya dauki alkawura

Sanarwar ta kuma bayyana cewa Gwamna Radda ya umarci ma’aikatar ayyuka da ta tafi ta kimanta hanyar Mantau tare da tsara shirin gina sabuwar makaranta da asibiti.

Ya kara da yin alkawarin gyaran masallacin da aka lalata, sake gina gidajen da aka kona da kuma bayar da tallafi ga iyalan waɗanda suka rasu.

Gwamna Radda ya kai ziyara kauyen Mantau
Gwamna Dikko Umaru Radda tare da jami'an tsaro yayin ziyarar da ya kai a kauyen Mantau Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Gwamna Radda ya sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

"Za mu ci gaba da kare rayuka da dukiya. Tsaro al’amari ne na rayuwar ɗan adam, ba na siyasa ba. Da goyon bayan jama’armu, In Sha Allah, za mu yi nasara."

- Gwamna Dikko Radda

Gwamna Radda ya magantu kan rashin tsaro

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda, ya yi magana kan matsalar rashin tsaron da ta addabi jihar.

Gwamna Radda ya nuna takaicinsa kan yadda ake samun sakaci a wasu lokutan daga bangaren jami'an tsaro idan aka tashi kawo hare-hare.

Ya koka kan cewa a matsayinsu na gwamnoni, wasu abubuwan sun fi karfinsu domin ba su da iko a kan sojoji ko 'yan sanda.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng