Kaduna: An Ɓarke da Murna bayan Mutuwar Hatsabibin Ɗan Daba da Ya Addabi Bayin Allah

Kaduna: An Ɓarke da Murna bayan Mutuwar Hatsabibin Ɗan Daba da Ya Addabi Bayin Allah

  • Mutane da dama suna ta murna bayan tabbatar da mutuwar wani rikakken dan daba a Kaduna da ke Arewacin Najeriya
  • Rahotanni daga Kaduna sun tabbatar da mutuwar sanannen ɗan daba abin da ya jawo martani daban-daban a yankin
  • Wasu mazauna unguwar sun nuna farin ciki da mutuwarsa saboda zargin cin zarafi, yayin da wasu suka yi jimamin mutuwar tasa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kaduna - Rahotanni daga jihar Kaduna sun tabbatar da mutuwar sanannen ɗan daba wanda ya addabi al'umma da dama.

Majiyoyi sun bayyana cewa al'ummar yankin da dan daban ya fito sun nuna farin ciki kan lamarin da ya faru.

Gwamnati na daukar matakai kan yan daba a Kaduna
Gwamnan Kaduna, Uba Sani yayin taro a jihar. Hoto: Uba Sani.
Source: Facebook

Rahoton Zagazola Makama ya ce dan daba, Abubakar Sadiq wanda aka fi sani da Habu Dan Damisa ya yi bankwana da duniya.

Kara karanta wannan

An rage mugun iri, jami'an DSS da sojoji sun hallaka rikakkun ƴan bindiga 50

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda 'yan daba ke addabar jihohin Arewa

Hakan na zuwa ne yayin da jihohin Arewacin Najeriya ke fama da hare-haren yan daba wanda ke jawo rasa rayuka da dukiyoyi.

Kaduna ma ba a bar ta a baya ba, yan daba na cin karensu babu babbaka a wasu yankunan jihar.

'Yan daba sun kashe soja a Kaduna

Ko a kwanakin baya, wasu miyagun matasa sun jawo asarar ran babban jami’in sojan ruwa Commodore M. Buba a lokacin da suke kici-kicin kwace masa waya.

An tabbatar da cewa M. Buba ya tsaya domin gyara tayar motarsa da ta samu matsala a Kawo ta jihar Kaduna a lokacin da lamarin ya afku.

An ga wasu matasa sun bi ta kan jami'in suna kokarin kwace masa masa da sauran kayan da take tafe da shi, amma rikici ya kaure a tsakaninsu.

An tabbatar da mutuwar dan daba a Kaduna
Taswirar jihar Kaduna da ke Arewa maso Yammacin Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Wasu sun yi murna bayan mutuwar 'dan daban

Mutuwar matashin, ɗan unguwar Tudun Wada a Kaduna, ta faru ne ranar Laraba 27 ga watan Agustan 2025 da muke ciki.

Kara karanta wannan

Gwamna ya kara albashi, wasu ma'aikata za su samu rabin miliyan a wata

An tabbatar da cewa mutuwar ta jawo martani daban-daban tsakanin mazauna yankin.

Yayin da wasu mazauna suka nuna farin ciki, suna murnar labarin rasuwarsa, wasu kuma sun nuna tausayin da kukan rashin rashin da aka yi.

“An zarge shi da cin zarafi a unguwa tare da zargin kashe mutane da dama.
"Amma abin kawai shi ne mu ce Allah ya gafarta wa mamatanmu kuma ya shiryar da zuriyarmu."

- Cewar wani mazaunin yankin

Rahoton ya tabbatar cewa Dan Damisa ya kasance matashin da aka fi tsoro a yankin.

Hakan ya jawo murna daga wasu ɓangarori saboda ya gudanar da rayuwarsa cikin tayarwa al'umma hankali.

'Yan sanda sun hallaka 'dan daba a Kano

A baya, mun ba ku labarin cewa rundunar ƴan sanda a jihar Kano ta kawo ƙarshen ayyukan ta'addancin wani tantirin ɗan daba da ake kira Baba Beru.

Ƴan sandan sun hallaka Baba Beru ne bayan ya yi yunƙurin farmakarsu da wuƙa lokacin da suke je kama shi a jihar Kano.

Baba Beru dai ya gamu da ajalinsa ne a ranar Talata, 22 ga watan Afirilun 2025 a unguwar Gwammaja da ke birnin Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.