"Ku Yafe Mani," An Ji Wanda Ya 'Jawo' Hatsarin Jirgin Kasan Kaduna zuwa Abuja da

"Ku Yafe Mani," An Ji Wanda Ya 'Jawo' Hatsarin Jirgin Kasan Kaduna zuwa Abuja da

  • Hatsarin da jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ya yi a jiya Talata, 26 ga watan Agusta, 2025 ya ja hankalin yan Najeriya
  • Hukumar NRC ta dakatar da harkokin sufurin jiragen kasa a layin dogon Abuja zuwa Kaduna, ta fara bincike don gano abin da ya jawo hatsarin
  • Shugaban NRC na kasa, Kayode Opeifa ya dauki alhakin abin da ya faru tare da tabbatar wa yan Najeriya cewa hakan ba za ta sake aukuwa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban hukumar kula da harkokin sufurin jiragen kasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa, ya dauki duka laifin hatsarin da ya faru a layin dogon Abuja zuwa Kaduna.

Kayode Opeifa ya kuma nemi afuwar yan Najeriya kan hatsarin da jirgin kasan ya yi a hanyarsa ta zuwa Kaduna ranar Talata, lamarin da ya jikkata fasinjoji shida.

Kara karanta wannan

Sarkin Kano, Sanusi II ya jagoranci wasu shugabannin duniya zuwa gidan Buhari

Shugaban NRC, Kayode Opeifa.
Hoton wurin da jirgin kasa ya yi hadari a Kaduna da Shugaban NRC na kasa, Kayode Opeifa Hoto; @KayodeOpeifa
Source: Twitter

Mista Opeifa ya bayyana hakan ne a lokacin da ya halarci shirin The Morning Brief na tashar Channels Television a ranar Laraba, 27 ga watan Agusta, 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kuma tabbatar da cewa tuni aka fara gudanar da bincike kan lamarin kuma ba za a boye wa jama'a komai ba.

Idan ba ku manta ba, jirgin kasa ya gamu da hatsari yayin da ya sauka daga kan layin dogo a hanyarsa ta zuwa Kaduna bayan ya baro Abuja jiya Talata.

Shugaban NRC ya dauki alhakin hatsarin jirgi

Da yake martani kan hatsarin jirgin kasan, shugaban NRC ya ce:

“Ba ya ga neman afuwar ‘yan Najeriya, ina so in bayyana cewa a matsayina na darakta kuma shugaban hukumar NRC, na dauki alhakin abin da ya faru. Idan abu ya shafi tsaro, babu sakaci.
“Da zarar abu ya faru, shugaba ne ya kamata ya dauki alhaki. A wannan yanayin, ni na dauki alhaki."

Kara karanta wannan

Ta faru ta ƙare: Hukumar jiragen ƙasa ta dakatar da zirga zirga daga Kaduna zuwa Abuja

Wane mataki hukumar NRC ta dauka?

Sai dai ya kara da cewa, duk da tun farko bai kamata lamarin ya faru ba, amma hukumar NRC za ta tabbatar irin wannna hatsarin bai sake faruwa ba, rahoton Tribune.

“Ba mu yi tsammanin afkuwar irin wannan lamari ba, ba mu fatan ya faru, bai kamata ya faru ba, amma idan ya faru, ya ba mu damar mu nuna kwarewarmu.
“Kuma ina tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa kamar yadda muke yi a layin dogon Warri-Itakpe, wadda kuka ji ya ambata, mun rufe hanyar kimanin makonni uku da suka gabata.
“Na bayar da umarnin rufe ta saboda dalilan tsaro, kuma idan kuka ga irin aikin da ma’aikata ke yi a kan layin dogon, suna cire karafan titin su na canza sababbi, duk domin tabbatar da irin wannan abu bai sake faruwa ba."

- Kayode Opeifa.

Hatsarin jirgin Kasuna.
Hoton wurin sa jirgin kasa ya sauka daga kan titinsa a Abuja-Kaduna Hoto: @zagazolamakama
Source: Twitter

Fasinjoji 6 sun ji rauni a hatsarin jirgin Kaduna

A wani rahoton, kun ji cewa an tabbatar da cewa fasinjoji shida sun ji raunuka sakamakon hatsarin jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja.

Kara karanta wannan

Duk da yana Brazil, Shugaba Tinubu ya yi magana kan hatsarin jirgin kasan Kaduna

Hukumar NSIB ce ta tabbatar hakan, amma ta bayyana cewa babu wanda ya rasa ransa sakamakon hatsarin jirgin kasan.

NSIB ta tabbatar da cewa ta tura tawagar bincike zuwa wurin da lamarin ya faru domin tattara shaidu da tattaunawa da masu ruwa da tsaki.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262