Sarkin Kano, Sanusi II Ya Jagoranci Wasu Shugabannin Duniya zuwa Gidan Buhari

Sarkin Kano, Sanusi II Ya Jagoranci Wasu Shugabannin Duniya zuwa Gidan Buhari

  • Ana ci gaba da zuwa yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta'aziyya tun bayan rasuwar tsohon shugaban kasar a watan Yuli, 2025
  • Mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya jagoranci tawagar shugabannin Fulani na duniya zuwa gidan Buhari a Kaduna
  • Wannan ne karo na biyu da Sanusi II ya je gidan Buhari yin ta'aziyya tun bayan dawowarsa Najeriya saboda bai halarci jana'iza ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna - Mai martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya sake komawa karo na biyu gidan marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke Kaduna.

Sarki Sanusi II, Khalifan Tijjaniyya a Najeriya ya raka shugabannin kungiyar Fulani ta duniya zuwa gidan Buhari domin yi wa iyalansa ta'aziyya.

Sarki Muhammadu Sanusi II.
Hoton Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II tare da tawagar fulani a gidan Marigayi Muhammadu Buhari Hoto: @masarautarkano
Source: Twitter

Masarautar Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya ta tabbatar da hakan a wata gajeruwar sanarwa tare da hotuna da ta wallafa a shafin X yau Talata, 26 ga watan Agusta, 2025.

Kara karanta wannan

'Kowa ya shirya,' Ana fargabar ambaliya za ta shafi yankuna 14 a jihohin Arewa 9

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rasuwar Buhari da abin da ya biyo baya

Wannan dai na zuwa ne kwanaki kadan bayan cikar shugaba Buhari kwanaki 40 da rasuwa, inda aka yi taron addu'o'in sake nema masa gafara da rahamar Allah.

Idan ba ku manta ba, tsohon shugaban kasar ya rasu ne a ranar 13 ga watan Yuli, 2025 a wani asibiti da ke birnin Landan na kasar Birtaniya.

Rasuwar Muhammadu Buhari ta girgiza 'yan Najeriya da shugabanni, inda Gwamnatin Tarayya ta shirya masa jana'izar girmamawa a mahaifarsa, Daura.

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da kusan duka mukarrabansa, gwamnoni, yan Majalisa, sarakuna, 'yan kasuwa da dubban yan kasa sun halarci jana'izar Buhari.

Sarki Sanusi II bai je jana'izar Buhari ba

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II na cikin manyan Arewa da ba a gani a wurin jana'izar Buhari ba.

Hakan ta faru ne saboda basaraken ba ya gida Najeriya lokacin da Buhari ya rasu kuma har aka yi maaa sutura aka birne shi bai dawo ba.

Kara karanta wannan

JIBWIS ta ƙalubanci masu cewa an yi wa Jingir ihu a Abuja, ta sanya kyautar kuɗi

Bayan ya dawo Najeriya, Sanusi II ya sa an sauke tutar masarauta domin girmama marigayin, sannan kuma ya je gidansa na Kaduna ya yi wa iyalansa ta'aziyya.

Sarkin Kano da tawagar Fulani.
Hoton Sarkin Kano da shugabannin fulani a gidan Buhari da ke Kaduna Hoto: @masarautarkano
Source: Twitter

Sarkin Kano ya sake komawa gidan Buhari

A karo na biyu Sanusi II ya koma gidan Buhari, inda ya je tare da shugabannin kungiyar Fulani ta duniya da suka zo don jajantawa iyalan tsohon shugaban kasar.

Masarautar Kano ta ce:

"Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, CON, ya jagoranci tawagar Ƙungiyar Fulani ta Duniya zuwa Kaduna don yin ta’aziyya ga iyalan marigayi Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, yau Talata, 26 ga Agusta, 2025."

Sarki Sanusi II ya gana da Obasanjo a Legas

A wani labarin, kun ji cewa Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya ziyarci jihar Lagos kuma ya gana da tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo.

An tabbatar da cewa basaraken ya samu rakiyar wasu manya a masarautar ciki har da Waziri, Galadima da Magajin Garin Kano.

Sarki Muhammadu Sanusi II da Obasanjo sun tattauna kan muhimman batutuwa a ganawar da suka yi amma ba a fitar da cikakken bayani ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262