Ranar Hausa: Abubuwan da Ya Kamata Ku Sani yayin da Bikin 2025 Ya Kankama a Daura

Ranar Hausa: Abubuwan da Ya Kamata Ku Sani yayin da Bikin 2025 Ya Kankama a Daura

Daura, jihar Katsina - Yau Talata, 26 ga watan Agusta, ita ce ta ranar da ake bikin ranar Hausa ta duniya a kowace shekara.

An fara bikin wannan rana ne a shekara 2015 domin tunawa da al'adun Hausa, ci gaban harshen da kuma zamantakewar Bahaushe.

Ranar Hausa.
Hoton yadda bikin ranar Hausa ke gudana a Daura Hoto: Ahmed Daura
Source: Facebook

Wanene ya kirkiro ranar Hausa ta duniya?

Tsohon ma'aikacin Legit Hausa da BBC Hausa wanda yanzu haka yake aiki da TRT Hausa, Abdulbaki Aliyu Jari ne ya kirkiro ranar Hausa ta duniya a 2025.

Abdulbaki Jari ya fara fafatukar ranar Hausa ta duniya tare da hadin gwiwar wasu abokansa a shafukan sada zumunta, rahoton Daily Trust.

An kirkiro wannan rana ne domin hada duk masu magana da harshen Hausa wuri guda a tattauna kan ci gaban harshen da kuma kalubalen da yake fuskanta a karni na 21.

A cikin shekaru biyu da suka gabata, ana gudanar da bikin Ranar Hausa ta Duniya a fiye da kasashe 20, ciki har da Faransa da Saudiyya.

Kara karanta wannan

Babu zama: Kwankwaso ya dura Legas bayan ruguza kasuwar Hausawa

Bunkasar harshen Hausa a duniya

Abdulbaki Jari ya ce bisa ga binciken baya-bayan nan, harshen Hausa shi ne na 11 a jerin harsunan da aka fi amfani da su a duniya, kuma ana hasashen zai hau matsayi na biyar nan da 2050.

Masu fafutukar wannan rana suna fatan cewa nan gaba za a amince da yaren Hausa a hukumance a ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) da kuma ƙungiyar raya ƙasashen yammacin Afrika (ECOWAS).

A baya-bayan nan sai da hukumar Lafiya ta Duniya watau WHO ta sanya Hausa a cikin harsuna guda uku da ta zaɓa domin yaki da annobar korona a nahiyar Afirka

Ana kallon al'ummar Hausawa a matsayin ɗaya daga cikin ƙabilu masu muhimmanci a yammacin Afirka, da al’adunsu na musamman a faɗin nahiyar da ma sauran ƙasashen duniya.

Abdulbaki Jari.
Hoton fitaccen dan jarida, Abdulbaki Jari, wanda ya jagoranci kirkiro ranar Hausa ta duniya Hoto: Abdulbaki Jari
Source: Facebook

Manufar kirkiro ranar Hausa ta duniya

A wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, tsohon editan na Legit Hausa kuma wanda ya kirkiro ranar Hausa, Abdulbaki Jari ya ce za a yi bikin bana a garin Daura.

Kara karanta wannan

'Kowa ya shirya,' Ana fargabar ambaliya za ta shafi yankuna 14 a jihohin Arewa 9

Abdulbaki, wanda ya dauki bidiyon a gaban fadar sarkin Daura, ya ce ana shirya bikin ranar Hausa ne domin tunatar da muhimmanci harshen Hausa, al'adu da uwa uba hadin kai.

"Rana ba ta karya, yau Talata, 26 ga watan Agusta, 2025 ita ce ranar Hausa ta duniya, kuma ga mu a fadar Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Farouk Umar, CON, fadar Hausa.
"A nan fadar mai martaba za a gudanar da bikin ranar Hausa ta duniya, taro ne da ake yi domin tunatar da mu muhimmancim harshenmu, al'adarmu da uwa uba hadin kan al'ummar mu."
"Ku zo Daura domin ganin tantagaryar al'adar Hausawa da kuma baiwar da Allah ya yiwa Malam Bahaushe daga al'adunsa, harshensa da kuma yanayin zamantakewa.

- Abdulbaki Jari.

Bikin ranar Hausa ya kankama a Daura

A bana an shirya bikin wannan rana a garin Daura da ke jihar Katsina a Arewa maso Yammacin Najeriya. Ana ganin Daura a matsayin tushen Hausa.

Rahotanni sun nuna cewa yanzu haka bikin ranar Hausa ya kankama a Daura, jihar Katsina, inda manyan mutane daga ciki da wajen Najeriya suka halarta.

Kara karanta wannan

'Lokaci ya yi da za a dauki mataki,' ACF ta shiga takaicin yadda ake zubar da jinin 'yan Arewa

Bikim ranar Hausa.
Hoton Sarkin Daura lokacin da ya tarbi gwamna da Sarkin Damagaran a wurin bikin ranar Hausa Hoto: Aminiya
Source: Twitter

Aminiya ta rahoto yadda makada da mawaka ke nuna bajintarsu da kayatar da mahalarta taron da al'adun Hausa iri daban-daban.

Manyan baki daga ciki wda wajen Najeirya sun hallara a kofar fadar Sarkin Daura albarkacin wannan rana mai matukar muhimmanci ga Hausawa.

Daga cikin wadanda suka halarci bikin ranar Hausa a Daura akwai gwamnan Damagaran, Kanar Yosouf Labo da kuma Sarkin Damagaram, Aboubacar Sanda Oumarou.

Bikin ranar Hausa a jami'o'in Najeriya

Haka kuma bikin wannan rana za ta gudana a jami'o'i musamman wadanda ake karantar da harshen Hausa irinsu jami'ar Ahmadu Bello a Zariya.

A bikin wannan shekara, za a karrama Farfesa Dalhatu Muhammad wanda ya bada gagarumar gudumuwa wajen bunkasar harshen a Najeriya.

Sarkin Daura ya koka kan sare itatuwa

A wani labarin, kun ji cewa mai martaba Sarkin Daura ya nuna damuwarsa kan yadda mutane ke sare itatuwaba bisa ka'ida ba a jihar Katsina.

Kara karanta wannan

Kano: Jami'an NDLEA sun cafke matashi da tramadol 7,000 daga Legas

Sarkin ya ce sare itatuwa ba tare da bin ka’idojin da ya kamata ba ya fi ta’addanci saboda barazanar da yake wa muhallin da al'umma ke rayuwa a ciki.

A cewar Mai Martaba Umar Farouk Umar, majalisar masarautar ta dauki sare itatuwa a yankin a matsayin babban laifi saboda hadarinsa ga al’umma.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262