Maza Sun Gaza Ne?, ‘Dalilin da Ya Sa Ya Kamata Mace Ta Mulki Najeriya a Yanzu’

Maza Sun Gaza Ne?, ‘Dalilin da Ya Sa Ya Kamata Mace Ta Mulki Najeriya a Yanzu’

  • Yar takarar shugaban ƙasa, Ada Kate Uchegbu, ta ce Najeriya na buƙatar mace shugaba don kawo sabon salo da ci gaban ƙasa
  • Ta jaddada cewa sake-sake shugabanni ya gaza, mace shugaba za ta kawo sauyi, inganci, da ƙarfin matasa wajen gyaran ƙasa
  • Uchegbu ta ce za ta yaƙi cin hanci da rashin tsaro, ta kuma kafa shirin samar da aikin yi ga matasa da sauya siyasar ƙasa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Yayin da ake shirye-shirye musamman kan zaben 2027 da ke tafe, wasu sun fara kiran ba mace damar zama shugabar kasa.

Yar takarar shugaban ƙasa, Ada Kate Uchegbu, ta bayyana cewa Najeriya na bukatar mace shugaba domin kawo sabon salo na shugabanci.

An bukaci ba mata dama domin shugabantar Najeriya
Tsofaffin shugaban kasar Najeriya, Jonathan, Buhari, Tinubu. Hoto: Goodluck Jonathan, Muhammadu Buhari, Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Facebook

2027: Yar takara ta bukaci ba mata dama

Uchegbu ta jaddada cewa Najeriya ta gaji shugabanni iri ɗaya da ake maimaitawa, abin da bai haifar da ci gaba ba, cewar Tribune.

Kara karanta wannan

2027: Atiku ya ba da ƙafa, ya faɗi abin da ya sa yake takarar shugaban ƙasa

Ta ce lokaci ya yi da ya kamata a samu sauyi a Najeriya inda ta tabbatar da cewa mace shugaba za ta kawo sauyi a Najeriya.

A cewar ta, mata na daga cikin shugabanni mafi ƙarfi a Afirka, sun cancanci jagoranci ba wai kawai don nuna bambancin jinsi ba, amma saboda ƙwarewa.

Ta ce idan mace ta zama shugaban ƙasa, za a ga sabon salo a tsarin siyasar ƙasa da Afirka baki ɗaya, wannan zai wargaza tsohon tunanin da ake yi.

Yar takarar shugaban kasa ta bayyana cewa burinta shi ne kawo sauyi na ƙarni, duba da shekaru da tunani, ta ce ƙasa na bukatar sababbin ra’ayoyi da shugabanni.

Yar takara ta nemi ba mace damar zama shugabar kasa
Bola Tinubu yana shekara ta 2 a mulkin Najeriya. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Facebook

Yar takara ta fadi jajircewar mata a shugabanci

Uchegbu ta ce gogewarta a aikin jarida ta koya mata yadda manufofi ke shafar rayuwar mutane, hakan ya ƙarfafa mata hangen nesa na gaskiya da riƙon amana.

Ta kuma gargadi al’ummar Anambra da su zaɓi cancanta ba kuɗi ko manyan masu goyon baya ba, ta ce cancanta ce mabuɗin ci gaban ƙasa.

Kara karanta wannan

Obasanjo ya kara rubuta littafi, ya fallasa aika aikar alkalai a Najeriya

Uchegbu ta bayyana cewa matsalar mata ba ta ƙwarewa ba ce, illa tsarin siyasa mai cike da wariya.

Alkawuran da yar takarar shugaban kasa ta yi

Haka kuma, ta yi alƙawarin yaƙi da tsaro ta hanyar sake fasalin hukumomi, amfani da fasaha, da samar da rukunin mata a cikin jami’an tsaro.

Ta kuma ce za ta ƙaddamar da shirin samar da aikin yi ga matasa da asusun tallafi, inda ta jaddada cewa matasa su ne makomar ƙasa.

'Tinubu zai laseh zaben 2027' - Jigon APC

Mun ba ku labarin cewa wani babban jigon APC, Farfesa Haruna Yerima, ya bayyana cewa Bola Tinubu zai yi nasarar 2027 idan ya cigaba da tafiya da Kashim Shettima.

Kungiyar Northern Ethnic Nationality Forum ta bukaci Tinubu ya sauya Shettima, inda ya ce ikirarin tsoron Musuluntarwa karya ne.

Yerima ya kara da cewa Shettima ya cancanta, kuma Tinubu ba karamin ɗan siyasa ba ne da za a tilasta masa mataimaki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.