An Dauki Gwamna 1 a Najeriya, An ba Shi Lambar Yabo Ta 'Zabin Jama'a' a Kasar Faransa

An Dauki Gwamna 1 a Najeriya, An ba Shi Lambar Yabo Ta 'Zabin Jama'a' a Kasar Faransa

  • An bai wa Gwamna Bala Mohammed lambar yabo a kasar Faransa bisa yadda ya kawo sauyi a harkokin shugabancin jihar Bauchi
  • Gwamnan ya shiga cikin jerin gwamnonin kasashen Afirka da suka samu lambar yabon People’s Choice Governors Excellence Award a birnin Faris
  • Sanata Bala Mohammed ya ce wannan girmamawa za ta kara zaburar da shi wajen kawo manufofin da za su inganta rayuwar yan Bauchi

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Bauchi - Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya samu lambar yabo ta zabin jama'a, 'People’s Choice Governors Excellence Award' a birnin Faris na kasar Faransa.

An karrama Gwamna Bala ne tare da gwamnoni tara daga nahiyar Afirka domin yaba masu bisa kyakkyawan jagorancin da suka kafa a jihohinsu.

Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi.
Hoton Gwamna Bala Mohammed a fadar gwamnatin Bauchi Hoto: @SenBalaMohammed
Source: Facebook

Mai magana da yawun gwamnan Bauchi, Mukhtar Gidado ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai jiya Alhamis, kamar yadda Leadership ta rahoto.

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: Shugaban Boko Haram, Bakura ya karyata labarin kashe shi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda aka ba Gwamna Bala lambar yabo

Ya bayyana cewa lambar yabon da aka bayar a rukunin nahiyar Afirka, ta zakulo shugabannin da suka kawo sauyi da jagoranci mai nagarta ga al'umarsu.

A cewarsa, wannan lambar yabo ta zo ne a matsayin girmamawa ga tsare-tsaren gwamnan da suka kunshi inganta rayuwar jama’a, samar da ayyukan raya kasa, da tabbatar da shugabanci nagari.

Shugaban ma'aikatar fadar gwamnatin Bauchi, Dr. Aminu Hassan Gamawa ne ya wakilci Gwamna Bala a wurin bikin mika wadannan kyaututtuka a birnin Faris.

Jawabin da gwamnan ya yi a Faransa

A jawabin da ya isar ta bakin wakilinsa, gwamnan ya bayyana wannan karramawa a matsayin kira na kara dagewa wajen yi wa Bauchi hidima.

Ya ce:

“Wannan kyauta tana tunatar da mu cewa, duk wani ci gaba da muka samu a yau shi ne kakkarfan ginshikin ci gaban gobe. Ba wai game da mukami ko siyasa ba ne, sai dai tasirin abin da za mu bari.”

Kara karanta wannan

Nijar: An harbe shugaban Boko Haram da ya maye gurbin Shekau har lahira

Ya yi godiya ga masu shirya bikin saboda adalcinsu da jajircewarsu wajen haskaka shugabannin da ayyukansu ke kawo canji mai kyau a nahiyar Afirka.

An karrama gwamnoni 10 daga Afirka

Bikin na Paris ya samu halartar shugabanni, masana tsare-tsare, da masu fafutukar ci gaba, inda gwamnoni 10 daga kasashen Afrika, ciki har da Kenya, Masar, Morocco, Habasha, da Najeriya, suka samu lambar yabo.

Gwamna Bala ya jaddada manyan nasarorin da gwamnatinsa ta samu, ciki har da gina sabbin hanyoyi da gine-ginen zamani, gyaran makarantu da cibiyoyin kiwon lafiya a kananan hukumomi 20.

Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi.
Hoton Bala Mohammed lokacin da aka karrama shi da wasu kyaututtuka a fadar gwamnatinsa Hoto: @SenBalaMohammed
Source: Twitter

Haka kuma, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta rungumi hadin kai da zaman lafiya a matsayin mabuɗin ci gaban Bauchi, rahoton The Sun.

Gwamnan ya kuma gayyaci kasashen duniya su halarci taron zuba jari na Bauchi mai zuwa, inda za a nuna damammaki a fannonin noma, gine-gine, ma’adinai, fasaha da yawon bude ido.

Gwamnan Bauchi ya ba dan China mukami

A wani rahoton, kun ji cewa Gwamnan Bala Mohammed ya nada ɗan ƙasar China, Li Zhensheng, a matsayin mai ba shi shawara kan tattalin arziki.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta bullo da shirin afuwa ga 'yan daba, ta fadi wadanda za su amfana

Gwamna Bala ya bayyana hakan ne a wurin taron rattaba hannu kan wata yarjejeniya tsakanin gwamnatin Bauchi da cibiyar CGPCRC.

Bala Mohammed ya ce wannan matakin da ya dauka zai sanya Bauchi ta zamo a gaba gaba wajen kulla alaka da kasashen duniya don samar da ci gaba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262