'Akwai Sharadi,' Gwamnati Za Ta Fara ba Ma'aikatan Manyan Makarantu Bashin N10m

'Akwai Sharadi,' Gwamnati Za Ta Fara ba Ma'aikatan Manyan Makarantu Bashin N10m

  • Gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da asusun TISSF domin ba malamai da ma’aikatan manyan makarantu rancen kuɗi marar ruwa
  • Gwamnati ta ce ma'aikatan za su iya amfani da kudin don kula da lafiya, biyan kudin haya, noma, kasuwanci da sauran bukatun rayuwa
  • Ma’aikatan manyan makarantu da suke da sauran shekaru biyar kafin ritaya ne za su iya neman bashin da ya kai Naira miliyan 10

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Gwamnatin tarayya ta kaddamar da asusun tallafawa ma'aikatan manyan makarantu (TISSF) da zai rika ba ma'aikatan rancen kudi marar ruwa.

An kaddamar da asusun TISSF ne domin bunkasa walwalar ma'aikata da kuma kara masu kwarin gwiwa wajen ci gaba da yi wa ilimi hidima.

Minisatan ilimi ya sanar da kaddamar da asusun ba da lamuni marar ruwa ga ma'aikatan manyan makarantu
Ministan ilimi, Tunji Alausa tare da jami'an ma'aikatar ilimi sun kaddamar da shirin horo na TVET. Hoto: @DrTunjiAlausa
Source: Twitter

Gwamnati ta kaddamar da asusun TISSF

Ministan ilimi, Dr. Tunji Alausa ne ya kaddamar da wannan asusu a wani taro da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis, kamar yadda Leadership ta ruwa.

Kara karanta wannan

Jerin sunaye: Shugaba Tinubu ya amince da kafa sababbin jami'o'i 9 a Kaduna da wasu jihohi 7

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dr. Tunji Alausa ya bayyana wannan asusu a matsayin wata kafa ta ba malamai da ma'aikatan manyan makarantu rancen kudin da suke bukata don gudanar da rayuwarsu cikin mutunci.

Ministan ya bayyana cewa asusun TISSF na karkashin shirin Renewed Hope na Shugaba Bola Tinubu da zummar daga darajar bangaren ilimi.

Ya ce an samar da asusun domin gina al'umma domin su ne babban jarin kasa wajen sauya fasalin ilimi da kuma ci gaban tattalin arziki.

A cewar ministan, ma'aikatar ilimi ta tarayya da kuma asusun TETFund ne suka samar da shirin tallafin tare da hadin gwiwar Bankin Masana'antu (BoI).

Amfanin ba da rance ga ma'aikatan makarantu

Punch ta rahoto cewa a karkashin wannan shirin, gwamnati ta bayyana wasu dalilai da take fatan malamai da ma'aikatan manyan makarantu za su nemi rancen kudin.

"Malamai da ma'aikatan manyan makarantu za su iya neman rancen kudin domin biyan kudin magani ko kula da kiwon lafiyarsu da ta iyalansu, da kuma biyan kudin haya.

Kara karanta wannan

Ana batun rashin lafiyar Tinubu, Gwamna Radda zai tafi jinya domin duba lafiyarsa

"Hakazalika, za su iya yin amfanin da kudin don harkokin zirga-zirga (da ya hada da sayen motocin lantarki ko sauya motocinsu na fetur zuwa na CNG).
"Hakakuma, masu neman bashin za su iya amfani da kudin don fara kasuwanci ko noma, da kuma fadada iliminsu ta hanyar ci gaba da karatu ko halartar shirye-shirye.

- Ministan ilimi, Tunji Alausa.

Ministan ilimi Tunji Alausa ya ce malamai da ma'aikatan manyan makarantu za su iya neman rancen N10m.
Ministan ilimi, Dr. Tunji Alausa yana jawabi a taron KADA EduPACT da aka gudanar a Kaduna a 2025. Hoto: @DrTunjiAlausa
Source: Twitter

Ma'aikatan makarantu za su samu lamunin N10m

Ministan ya kuma bayyana cewa shirin ya shafi dukkanin ma'aikatan jami'o'in tarayya, kwalejojin fasaha da na ilimi da tarayya da ma wasu manyan makarantun jihohi.

Ya kuma ce dole ne wadanda za su nemi rance su kasance suna da sauran akalla shekaru biyar kafin ritaya, kuma su zama mambobi a kungiyoyi irinsu ASUU, NASU, COEASU, da SSANIP.

"Wadanda suka cancanta za su iya neman rancen kud da suka kai N10m, amma za a kayyade hakan ga kashi 33.3 na albashinsa.
"Za a biya bashin kudin ne a tsawon shekaru biyar, kuma za a fara cire kudin bayan watanni 12 da karbarsu, ba tare da an cire kudin ruwa na ko sisin kwabo ba."

Kara karanta wannan

Ana batun sulhu, yaran Bello Turji sun harbe mutane a Sokoto, sun sace mutum 16

- Ministan ilimi, Tunji Alausa.

Za a dauki ma'aikata a manyan makarantu

A wani labarin, mun ruwaito cewa, gwamnatin tarayya za ta ɗauki sabbabin ma'aikata a manyan makarantu domin cike gurabe da giɓin da ake da su.

Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya umarci makarantun da aka ba izinin ɗaukar ma’aikata su sanar da guraben aikin da suke nema ta hanyar talla ga jama'a.

Ana ganin wannan umarni na ministan ilimin yana da nufin tabbatar da an bi tsarin ɗaukar aiki na gaskiya, ba da dama ga kowa, da kuma yin adalci yayin tantancewa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com