Boko Haram: Gwamna Zulum Ya Mika Bukatarsa ga Rundunar Sojojin Sama

Boko Haram: Gwamna Zulum Ya Mika Bukatarsa ga Rundunar Sojojin Sama

  • Babagana Umara Zulum, na son rundunar sojojin sama ta murkushe mayakan kungiyoyin ta'addanci na Boko Haram da ISWAP
  • Farfesa Zulum ya yi kira ga rundunar da ta tura jiragen yaki maboyar 'yan ta'adda da ke da wahalar shiga ga dakarun sojojin kasa
  • Gwamna Zulum ya kuma yi alkawarin ba da goyon bayan da ake bukata don samun nasarar ayyukan jami'an tsaro a jihar

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Borno - Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya mika kokon bararsa ga rundunar sojojin sama ta Najeriya (NAF) kan mayakan Boko Haram da ISWAP.

Gwamna Zulum ya bukaci rundunar da ta tura jiragen yaki domin kawar da mayakan Boko Haram da ISWAP daga wuraren da ke da wahalar shiga kamar tafkin Chadi, dajin Sambisa, Timbuktu Triangle da tsaunukan Mandara.

Kara karanta wannan

'Yan majalisa sun kai karar Gwamna Dauda kan matsalar rashin tsaro

Gwamna Zulum ya mika bukatarsa ga sojoji
Gwamna Zulum na son sojojin sama su murkushe 'yan Boko Haram Hoto: @NigAirforce
Source: Twitter

Gwamna Zulum ya bayyana hakan ne yayin da yake karɓar bakuncin babban hafsan sojojin sama (CAS), Air Marshal Hassan Bala Abubakar, a Maiduguri ranar Talata, 12 ga watan Agustan 2025, cewar rahoton jaridar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Zulum na son a kakkabe Boko Haram

Gwamna Zulum ya ce waɗannan wurare na yi wa sojojin kasa matukar wahalar tsarewa yadda ya kamata.

"Duk da irin gudunmawar da NAF ta bayar wajen tabbatar da zaman lafiya a Borno, har yanzu muna buƙatar ƙarin ƙarfin sojojin sama a yankin da muke da alhakin tsaro, musamman a sansanonin ‘yan ta’adda da ke wuraren da ba a iya shiga cikin sauki."

- Gwamna Babagana Umara Zulum

Gwamna Zulum ya yaba da tura jirage marasa matuƙi da sauran kayan aiki, tare da yin alkawarin ba da cikakken goyon bayan gwamnatin jihar domin tabbatar da nasarar ayyukan jami'an tsaro.

Haka kuma, ya jinjinawa haɗin gwiwa tsakanin NAF da sauran hukumomin tsaro wajen samun nasarori a yaƙin kawar da ‘yan ta’adda a baya-bayan nan, rahoton Daily Post ya tabbatar.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Zanga zanga ta barke a Kaduna, an ji abin da ya faru

Gwamna Zulum ya bukaci a kawo karshen Boko Haram
Gwamna Zulum ya yabawa rundunar sojojin sama Hoto: @ProfZulum
Source: Facebook

Shugaban sojojin sama ya yabi Zulum

A nasa jawabin, Air Marshal Abubakar ya yaba da irin jagorancin Gwamna Zulum da kuma tsarin “Borno Model” na dawo da ‘yan ta’adda cikin jama’a.

Sojan ya bayyana cewa wannan hanya ta zama nasarar magance ta’addanci ba tare da amfani da yaƙi kai tsaye ba.

Ya ce shirin tuba, ajiye makamai da dawo da su cikin jama’a, wanda ya fi mayar da hankali kan kai zuciya nesa da sulhu maimakon hukunci, ya inganta tsaro a fadin Borno da Arewa maso Gabas baki ɗaya.

Air Marshal Abubakar ya ƙara da cewa rundunar sojojin sama ta Operation Hadin Kai ta ƙara zafafa ayyukanta a bana fiye da yadda aka taɓa gani a baya.

'Yan Boko Haram sun kashe sojoji

A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan ta'addan Boko Haram sun kashe jami'an sojoji a wani hari da suka kai a Borno.

Kara karanta wannan

Danwawu: Abba ya fatattaki hadimi a Kano saboda hannu a belin dilan kwaya

'Yan ta'addan sun kai harin ne a kauyen Kirawa da karamar hukumar Gwoza, inda suka kuma yi awon gaba da wata daliba.

Harin na 'yan ta'addan ya sanya mutanen yankin tserewa zuwa kasae Kamaru domin tsira da rayukansu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng